Mawaki Zai Yi Tsirara Saboda Peter Obi Ya Yi Nasara a kan Bola Tinubu a Kotun Zabe

Mawaki Zai Yi Tsirara Saboda Peter Obi Ya Yi Nasara a kan Bola Tinubu a Kotun Zabe

  • Charles Oputa ya na cikin wadanda su ke goyon bayan Peter Obi, su ka tsaya masa a zaben 2023
  • Mawakin mai shekara 73 ya bayyana irin farin cikin da zai yi a duk ranar da LP tayi nasara a kotu
  • Jam’iyyar adawar da ‘dan takaranta su na shari’a a kotun zabe, su na neman a tsige Bola Tinubu

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Abuja - Shahararren matashin nan kuma mai gwagwarmaya, Charles Oputa wanda aka fi sani da Charley Boy ya dauki babban alkawari.

Charley Boy da yake magana a shafinsa na Twitter a makon nan, ya ce zai yi tunbur idan Peter Obi ya yi nasara a kotun sauraron karar zabe.

Peter Obi wanda ya yi takara a jam’iyyar LP ya na kalubalantar sakamakon zaben 2023 da Bola Ahmed ya lashe a karkashin APC mai-ci.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Shin Da Gaske Kotun Daukaka Kara Ta Sanar Da Peter Obi A Matsayin Wanda Ya Lashe Zabe? Bayanai Sun Fito

Peter Obi
Peter Obi yana ja da Bola Tinubu a kotun zabe Hoto: @PeterObi
Asali: Twitter

Saboda tsabagen farin ciki, idan LP za ta samu nasara a kotun da ke sauraron korafin zaben shugaban kasar, Oputa zai yi yawo tsirara a fili.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mawakin wanda yana cikin manyan magoya bayan Peter Obi ya ce zai yi zindir ne unguwar shugaban kasa Bola Tinubu a jihar Legas.

Alwashin Charley Boy

"Idan kotun sauraron karar zabe ta sanar da cewa Peter Obi ya yi nasara, tun kafinshari’ar ta kai kotun koli, me za ka yi a ranar?

Ni, zan yi yawo tsirara daga karshen unguwar Bodillon har zuwa Falomo [sic].”"

- Charley Boy

Kowa da irin salon da zai dauka

Mutane su na can su na ba Charley Boy amsa, daga masu cewa ga yadda za su yi murna, zuwa masu sukar matsayar da ya dauka.

Idan ya tashi nuna farin ciki, wani mai suna Holy Ghost ya ce kwanaki uku zai yi tsirara.

Kara karanta wannan

An Gama Komai, El-Rufai, Wike, Oyetola da Edun Za Su Zama Ministocin Bola Tinubu

Alara ya kawo shawarar cewa Charley Boy ya tara masu tukin babur, su cika Legas a ranar domin ayi farin ciki, a maimakon a fito zindir a titi.

Babu abin da mattobrown zai yi illa azumi da addu’ar farin ciki, amma @EzehNnamdiS ya ce zai ajiye aikinsa ne daga jin labarin.

Juyin mulkin Nijar

Kun ji labarin cewa tun tuni wani malamin addinin musulunci ya ce akwai yiwuwar a ga bayan Mohammed Bazoum a Jamhuriyyar Nijar.

Shugaban ya fara nuna zai juyawa Faransa baya ta hanyar buga kudi dabam da CFA, Aliyu Kaduna ya ce hakan zai zama karshen Bazoum.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng