Jerin Abubuwa 5 Da Obi Ya Bukaci Kotun Zabe Ta Yi Masa A Yayin Da Ya Ke Kallubalantar Nasarar Tinubu

Jerin Abubuwa 5 Da Obi Ya Bukaci Kotun Zabe Ta Yi Masa A Yayin Da Ya Ke Kallubalantar Nasarar Tinubu

FCT, Abuja - Peter Obi, dan takarar jam'iyyar LP na shugaban kasa, ya shigar da kara don kalubalantar nasarar Bola Tinubu na jam'iyyar APC a zaben 25 ga watan Fabrairun 2023.

Obi wanda ya yi na uku a zaben, ya shigar da kara don kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa a kotun sauraron karrarakin zabe a Abuja da yammacin Litinin, 20 ga watan Maris.

Tinubu da Obi
Peter Obi na Labour Party ya shigar da kara na kallubalantar nasarar Bola Tinubu a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu. Hoto: Photo credits: @OfficialABAT, @PeterObi
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ga jerin abu 5 da dan takarar jam'iyyar Labour ke nema a kotun:

1. A soke takarar Tinubu da Shettima

Obi ya roki kotun da ta ayyana Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima, a matsayin haramtattun yan takara a zaben 25 ga wata.

Ya kuma roki kotun da ta sanar da cewa Tinubu bai samu mafi rinjayen halastattun kuri'u ba a zaben.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: PDP ta yi jana'izar APC, ta lashe kujerar majalisa ta farko a jihar APC a Arewa

Na karshe, Obi ya bukaci kotun da ta bayyana shi (Obi) a matsayin wanda ya cika sharuddan da za a bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben 25 ga watan Fabrairu bayan kwashe haramtattun kuri'u daga na Tinubu

2. Kwace nasarar Tinubu saboda rashin samun kaso 25 a Abuja

A bukata ta biyu, tsohon gwamnan Jihar Anambra ya bukaci kotu ta kwace nasar Tinubu.

Ya kafa hujja da rashin samun Tinubu kaso daya bisa hudu na kuri'ar da aka kada a babban birnin tarayya, Abuja.

3. A soke zabe sannan a umarci INEC ta gudanar da sabo

A bukatarsa ta uku, wanda ya bari a matsayin zabi, Obi ya roki kotu da ta soke zabe gaba daya.

Ya kuma bukaci kotu ta umarci INEC ta sake gudanar da sabon zabe bayan ta soke wancan.

4. A bayyana ni a matsayin zababben shugaban kasa

Kara karanta wannan

Ba Za Ku Iya Kwace Wa Tinubu Nasarsa Ba, APC Ta Yi Martani Ga Obi

A bukatarsa ta hudu wanda ita ma ke a matsayin zabi, Obi ya yi ikirarin shi ya lashe zaben kuma ya na so kotun ta bayyana shi a matsayin zababben shugaban kasa.

Dan takarar jam'iyyar LP ya yi ikirarin cewa shi ya lashe mafi rinjayen halastattun kuri'un da aka kada a zaben 25 ga watan Fabrairu ya kuma bukaci kotu ta sanar da shi a matsayin zababben shugaban kasa ta kuma umarci INEC ta ba shi shaidar cin zabe.

Ya bukaci kotu ta soke shaidar cin zabe da aka baiwa Tinubu bisa ''kuskure''.

5. A soke zabe

A bukatarsa ta biyar, wani karin zabi, Obi ya bukaci kotu ta soke zabe a kuma sake wani zaben.

Ya kafa hujja cewa ya mika bukatar ne saboda an gudanar da zabe ba tare da bin dokokin zabe ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164