Zaben Shugaban Kasa: Yan Daba Sun Tarwatsa Masu Zabe a Wata Rumfar Zabe a Jihar Lagas

Zaben Shugaban Kasa: Yan Daba Sun Tarwatsa Masu Zabe a Wata Rumfar Zabe a Jihar Lagas

  • Jama'a sun shiga tashin hankali a yankin Ikate da ke jihar Lagas bayan wasu bata gari sun far masu a wajen zabe
  • Yan daban sun lalata tare da sace kayan zabe bayan sun fatattaki jama'a da jami'an hukumar zaben
  • A yau Asabar, 25 ga watan Fabrairu ne ake gudanar da zaben shugaban kasa da na yanmajalisun tarayya a fadin Najeriya

Lagos - Masu zabe a yankin Ikate da ke jihar Lagas basu samu damar aiwatar da yancinsu na yan kasa ba ta hanyar yin zabe a ranar Asabar, 25 ga watan Fabrairu.

Hakan ya kasance ne bayan wasu bata gari da ake zaton yan dabar siyasa ne sun farmaki rumfar zabensu sannan suka fatattaki jama'ar da suka taru domin yin zabe tare da lalata kayan zaben.

Jama'a sun yi cirko-cirko a wajen zabe
Zaben Shugaban Kasa: Yan Daba Sun Tarwatsa Masu Zabe a Wata Rumfar Zabe a Jihar Lagas Hoto: PM News
Asali: UGC

A cewar wasu da abun ya faru a kan idanunsu, lamarin ya shafi rumfar zabe ne da ke kusa da fadar sarkin Elegushi, jaridar Vanguard ta rahoto.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Yan Ta'adda Sun Kai Hari Rumfar Zabe, Sun Banka Wa Akwatin Zabe Wuta

Sai mun yi zabe za mu tafi, masu kada kuri'a

Sai dai kuma, masu kada kuri'ar da ke kokarin takewa yanci sun dage lallai sai sun aiwatar da yancinsu kafin su bar rumfar zaben.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

PM News ta kuma rahoto cewa rumfunan zabe hudu yan daban suka farmaka kuma hakan ya haifar da tashin hankali a yankin inda mutane suka dunga gudun tsira.

An kuma tattaro cewa maharan sun tsere da akwatunan zabe sannan suka fatattaki jami'an hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta.

Yan daba sun farmaki rumfar zabe a Kogi, sun bindige wani matashi

A wani lamari makamancin wannan, mun ji cewa wasu bata gari sun kai hari rumfar zabe a Anyigba da ke kamaramar hukumar Dekina ta jihar Kogi yayin da mutane suka taru don kada kuri'unsu.

Kara karanta wannan

Yan Daba Sun Fasa Akwatunan Zabe, Yan Sanda Sun Tarwatsa Kowa Da 'Tear Gas'

Maharan suna ta harbi kan mai uwa da wahabi inda aka yi rashin sa'a harbin bindiga ya samu wani matashi da ya je yin zabe tare da aika shi lahira.

Wannan tashin hankali da aka samu a yankin Kogi ta gabas ya yi sanadiyar da hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta, INEC, ta soke zabe a rumfunar zabe guda bakwai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng