Shugabancin Kasa A 2023: IBB Ya Goyi Bayan Atiku? Dino Melaye Ya Aike Da Sako Ga Tsohon Shugaban Mulkin Soja

Shugabancin Kasa A 2023: IBB Ya Goyi Bayan Atiku? Dino Melaye Ya Aike Da Sako Ga Tsohon Shugaban Mulkin Soja

  • Tsohon dan majalisar tarayya na Kogi, Dino Melaye, yana ikirarin cewa tsohon shugaban kasa na mulkin soja Ibrahim Badamasi Babangida yana goyon bayan Atiku Abubakar
  • Melaye ya bayyana godiyarsa ta tsohon shugaban mulkin sojan kuma ya bayyana labarin a shafin Facebook a ranar Juma'a, 27 ga watan Janairu
  • Tsohon sanatan ya ce Babangida ya bayyana matsayarsa kan ga kwamitin kamfen din Atikun ne ta hannun Mohammed Babangida a ranar Laraba, 25 ga watan Janairu

Jihar Delta - A cewar Dino Melaye, tsohon sanata daga jihar Kogi wanda ya wakilici Kogi ta Yamma, Ibrahim Badamasi Babangida ya goyi bayan takarar shugaban kasa na Atiku Abubakar a zaben da ke tafe.

Ta shafinsa na Facebook a ranar Juma'a, 27 ga watan Janairu, Melaye, mai magana da yawun kwamitin kamfen din shugaban kasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP, ya ce an tabbatar da hakan a Jihar Delta ranar Laraba, 25 ga watan Janairu, yayin kaddamar da wani aiki da Atiku ya yi.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: 'Dan Takarar Gwamna a Fitacciyar Jihar Arewa Ya Kwanta Dama Bayan Fama da Rashin Lafiya

Atiku da IBB
Shugabancin Kasa A 2023: IBB Ya Goyi Bayan Atiku? Dino Melaye Ya Aike Da Sako Ga Tsohon Shugaban Mulkin Soja. Hoto: (Photo: Dino Melaye)
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Melaye ya yi ikirarin cewa Babangida ya sanar da matsayinsa ta bakin dansa ne, Mohammed.

Wallafar na Melaye ta ce:

"Muna son mu gode wa iyalan tsohon shugaban kasa na mulkin soja Ibrahim Badamasi Babangida saboda goyon bayan Atiku a matsayin shugaban kasar Najeriya.
"Mohammed Babangida ne ya bayyana hakan a Jihar Delta a ranar Laraba yayin kaddamar da filin fina-finai da shakatawa na Maryam Babangida. Sanata Dino Melaye."

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164