Gwamnonin da Suka Yi Wa Atiku Bore Sun Karkata a Kan ‘Yan Takara 2 a Zaben 2023

Gwamnonin da Suka Yi Wa Atiku Bore Sun Karkata a Kan ‘Yan Takara 2 a Zaben 2023

  • Gwamnoni 5 da suka yi fito-na-fito da Atiku Abubakar a PDP za su goyi bayan wani ‘dan takara dabam
  • Ana tunani ‘Yan G5 za su fadawa magoya bayansu su zabi Peter Obi ko Bola Tinubu ne a zabe mai zuwa
  • Da alama Olusegun Obasanjo yana goyon bayan Obi, wasu kuma sun fi ganin cin ta ga jam’iyyar APC

London - Alamu masu karfi su na nuna Gwamnonin PDP biyar da ba su goyon bayan takarar Atiku Abubakar za su bayyana matsayarsu a kan zaben 2023.

Rahoton Punch na ranar Laraba, 28 ga watan Disamba 2022, ya nuna nan da 5 ga watan Junairun 2022, Gwamnonin jihohin za su sanar da ‘dan takaransu.

Ana tunanin tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo zai iya tasiri a kan zabin wadannan gwamnoni da yanzu su na taro a birnin Landan a Birtaniya.

Kara karanta wannan

An sanar da rana da wurin da Wike, gwamnonin G5 zasu sanar da dan takaran da zasu yi a 2023

Cif Olusegun Obasanjo yana da ra’ayin cewa kamata ya yi mulkin Najeriya ya koma yankin Kudu maso gabas a badi, ana zargin yana goyon bayan Peter Obi.

Obasanjo ya dage a kan LP

Watanni hudu da suka wuce, Obasanjo wanda ya mulki kasar nan tsakanin 1999 da 2007 ya zauna da wadannan Gwamnoni a Landan, ya tallata masu Obi.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Peter Obi yana neman takarar kujerar shugaban kasa a jam’iyyar hamayya ta LP. A cikin manyan ‘yan takaran 2023, shi kadai ya fito daga Kudu maso gabas.

Atiku Abubakar
Atiku Abubakar yana kamfe a Katsina Hoto: @Atiku
Source: Twitter

Hadimin wani daga cikin ‘Yan G5 ya shaidawa Punch cewa wasu daga cikin Gwamnonin nan na duba yiwuwar bin shawarar tsohon shugaban Najeriyar.

A ba Ibo mulki a 2023

Obasanjo yana ganin idan daga Kudu za a fito da shugaban kasa, kamata ya yi a je Kudu maso gabas, yankin da bai taba samun damar rike shugabanci ba.

Majiyar ta ce wannan shi ne abin da ya sa Obasanjo ya zauna da Gwamnonin a Landan a watan Agusta. A gefe guda ana tunanin wasu na goyon bayan APC.

Kara karanta wannan

Magoya Bayan Jonathan Sun Tsaida ‘Dan Takara, Sun Shiga Yi wa Tinubu Kamfe a Kudu

A saurari 5 ga watan Junairu

Har ila yau, majiyar ta bayyana cewa zuwa mako mai zuwa sa a wadanda abokan rigiman na Atiku Abubakar za su marawa baya a zaben shugabancin kasar.

A ranar 5 ga watan Junairun shekara mai zuwa, Gwamna Seyi Makinde zai kaddamar da yakin neman tazarce, a ranar ‘Yan G5 za su fito da ‘dan takararsu.

Wasu na kusa da Gwamnonin sun bayyana cewa babu sabani a kan goyon bayan ‘Dan Kudu ya karbi mulki tun da Atiku ya ki yarda a sauke shugaban PDP.

Kwankwaso ya ragargaji Atiku, Tinubu

An rahoto Rabiu Musa Kwankwaso yana cewa ya fi abokan gabansa ilmin boko, ya ce ana ta rigima a kan 'yan takaran sun yi sakandare, alhali shi yana da PhD.

‘Dan takaran Shugaban kasar a NNPP, ya ce masu takara da shi sun gaji, ba za su iya rike shugabanci ba. Kwankwaso yana nufin Bola Tinubu da Atiku Abubakar ne.

Kara karanta wannan

Ni Ba Safaya Taya Bane, Ba Na Amalala: Kwankwaso Ya Yi Shagube Ga Atiku da Tinubu

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng