Sanatoci Sun Dauko Aiki, Za a Ragewa Shugaban Kasa Iko Kan Nadin Shugaban EFCC

Sanatoci Sun Dauko Aiki, Za a Ragewa Shugaban Kasa Iko Kan Nadin Shugaban EFCC

  • Majalisar dattawa ta yi muhawara a kan kudirin da zai haramtawa shugaban kasa tsige shugaban hukumar EFCC
  • Idan kudirin ya samu shiga, shugaban kasa zai rasa damar tsige shugaba a EFCC ba tare da amincewar Sanatoci ba
  • Sanatan yankin Arewacin jihar Enugu, Chukwuka Utazi ya gabatar da kudirin, kuma yana ta samun karbuwa

Abuja - Kudirin da zai hana shugaban kasa tunbuke shugaban hukumar EFCC a Najeriya, ya tsallake matakin muhawara na biyu a majalisar dattawa.

A ranar Talata, 13 ga watan Disamba 2022, Premium Times ta ce an tattauna a kan wannan kudiri wanda zai rake karfin da doka ta ba shugaban Najeriya.

Kudirin yana kokarin canza dokar da ta kafa EFCC ta yadda dole a bukaci amincewar 'yan majalisar dattawa kafin shugaban kasa ya tsige shugaban hukumar.

Kara karanta wannan

Kowa ya huta: Atiku ya fadi yadda zai yi kungiyar ASUU idan ya gaji Buhari a zaben 2023

Sanata Chukwuka Utazi ya ce ya kawo kudirin domin daina wasa da wa’adin shugabannin EFCC. Abin da ya rage shi ne a tattauna a kai gaban kwamiti.

Idan Chukwuka Utazi ya yi nasara, nan gaba dole sai shugaban kasa ya samu rinjayen ‘yan majalisar dattawa kafin ya nada ko ya cire shugaba a EFCC.

Sanatan na Enugu ta Arewa yake cewa majalisar tarayya tayi kokari wajen ganin an hana shugaban kasa cire shugabannin hukumomin ICPC da NFIU kai-tsaye.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majalisa
Majalisar Dattawa Hoto: @NgrSenate / Tope Brown
Asali: Facebook

Abin ba haka yake a dokar EFCC ba, wannan ya sa mai tsawatar da marasa rinjaye a majalisar yake ganin za iyi kyau hukumar tayi koyi da sauran takwarorinta.

Za a hana dauko Shugaban EFCC a waje

Wata kwaskwarima da Sanatan yake so ayi ita ce a takaita shugabancin EFCC ga jami’in hukumar, ta yadda ba zai halatta a dauko shugaba daga waje ba.

Kara karanta wannan

Wata Kotu A Kano Ta Sanar Da Ranar Da Zata Yankewa Mallam Abdul-Jabbar Nasiru Kabara Hukuncin Kisa

A jawabinsa, ‘dan majalisar ya yabi Mai girma Muhammadu Buhari da wannan karo ya dauko ‘dan cikin gida (Abdulrasheed Bawa), ya rike masa hukumar.

Rahoton ya ce Sanatocin da suka tashi tofa albarkacin bakinsu, sun goyi bayan Utazi.

Sanata George Sekibo na gabashin Ribas yace garambawul din zai kawo gyara, wannan shi ne ra’ayin James Manager mai wakiltar kudancin jihar Delta.

Sam Egwu ya yabi Bawa, yace amma ba dole ba ne wanda zai gaje shi ya zama irinsa, don haka ba ya goyon bayan a ce dole daga hukumar za a samu shugaba.

Garba Shehu ya yi Kazaure raddi

An samu labari Malam Garba Shehu ya yi cikakken bayani kan tarihin nada kwamitin Muhammadu Gudaji Kazaure domin ya binciko satar kudi a CBN.

Hon. Kazaure ya ce N89tr ake zargin sun yi kafa, amma Hadimin shugaban kasar ya ce duka dukiyar da ke bankuna ba su kai rabin abin da Kazaure yake kira ba.

Kara karanta wannan

Fadar Shugaban Kasa: Kwamitin Gudaji Kazaure Haramtacce Ne, Ba Buhari Ne Ya Kafa Sa Ba

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng