'Tinubu Ya Kere Sauran Yan Takara Damar Lashe Zaben Shugaban Kasa a 2023'

'Tinubu Ya Kere Sauran Yan Takara Damar Lashe Zaben Shugaban Kasa a 2023'

  • Shugaban kwamitin yakin neman zaɓen shugaban kasa na APC a ƙasar Kanada ya yi hasashen Bola Tinubu ne zai lashe zaɓen 2023
  • Barista Jide Oladejo, yace Tinubu ne ɗan takara ɗaya tilo daga rukunin masu son gaje Buhari da ya gina tubalin nasara
  • Ya kuma yaba da kokarin gwamnati na kafa hukumar mazauna kasar waje amma yace suna jiran a fara basu damar kaɗa kuri'a

Akure, Ondo - Shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban ƙasa na jam'iyyar APC reshen ƙasar Kanada, Barista Jide Oladejo, yace damar Asiwaju Bola Tinubu na lashe zaben 2023 ta kere na sauran haske.

Jaridar The Nation ta ruwaito Oladejo na cewa Tinubu ya riga da ya gama duk wani shiri na zama shugaban kasa na gaba a Najeriya.

Bola Ahmed Tinubu.
'Tinubu Ya Kere Sauran Yan Takara Damar Lashe Zaben Shugaban Kasa a 2023' Hoto: Bola Tinubu
Source: UGC

Mista Oladejo, wanda ya zanta da manema labarai a Akure, yace Tinubu ya fita daban daga cikin masu hangen kujera lamba ɗaya, ɗan siyasar zamani wanda ya shirya inganta walwalar 'yan Najeriya.

Kara karanta wannan

Gwamna Ya Jingine Siyasa, Ya Bayyana Mutumin Da Ya Cancanci Zama Shugaban Kasa a 2023

Yace jam'iyyar APC a ƙasar Kanada zata wayar da kai kan kudirin Bola Tinubu domin tabbatar da ya samu nasarar raba ni da yaro a zaɓe mai zuwa.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A jawabinsa, Oladejo ya ce:

"Najeriya ƙasa ce mai ban sha'awa domin kowane ɗan kasa burinsa ya ɗare kan muƙamin shugabanci ba don komai sai don su yi wadaƙa da dukiyar al'umma."
"Sanata Tinubu na daban ne ɗan takara ne mai goshin nasara, zai lashe zaɓen shugaban ƙasa dake tafe don haka damarsa ta lashe zabe ta fi haske kan saura."
"Shi ne mutum ɗaya tilo daga cikin yan takara da ya kasance ɗan siyasar zamani, wanda ya haɗa kan kowa ya lashe tikitin APC kuma a shirye yake ya ƙara inganta rayuwar 'yan Najeriya."

Oladejo ya yaba da kafa hukumar 'yan Najeriya mazauna ƙasashen waje amma yace alfanunta na gaske ba zai cika ba sai an fara basu dama su kaɗa kuri'unsu a zaɓe.

Matasan Katsina Sun Yi Wa Atiku Alkawarin Kuri'u Miliyan Shida a Zaben 2023

Kara karanta wannan

2023: Atiku da Tinubu Sun Kara Shiri, Sun Yi Sabbin Naɗe-Naɗe a Kwamitin Yakin Neman Zabe

A wani labarin kuma Matan jihar Katsina sun sha alwashin yin duk me yuwuwa wajen haɗawa dan takarar PDP kuri'u miliyan 6m a zaɓen 2023

Matasa karkashin kungiyar Atiku Support Organization sun bayyana shirin da suke wa ɗan takarar shugaban kasa a PDP, Atiku Abubakar a jihar Katsina.

Kodinetan ƙungiyar, Yasir Ibrahim, ne ya bayyana haka yayin rantsar da Kodinetocin kananan hukumomi 34 dake faɗin jihar, waɗan zasu yi aiki don cika alƙawarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262