Karancin rajistar katin zabe a jihar Katsina ya ta da hankalin INEC
- Hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Katsina ta bayyana damuwarta kan yadda ake samu karancin rijistar katin zabe
- Kwamishinan INEC na jihar Katsina ya alakantar da karancin yin rajista da matsalar harkar tsaro da jihar ke fuskanata
- Zarewa ya ce kananan hukumomi 17 a jihar sunyi watanni biyar da yanke musu kafofin sadarwa
ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit
Katsina : Hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Katsina ta bayyana damuwarta kan yadda al,ummar jihar basa yin rijistar katin zabe na dindindin a sabbin rumfunan zabe 1,750 da aka kafa a jihar.
Kwamishina INEC na jihar, Alhaji Jibril Zarewa, ya bayyana haka a lokacin da ya zanatawa da manema labaran News Agency of Nigeria a ranar Juma’a kamar yadda PUNCH ta rawaito
Ya ce shakara daya kenan bayan kaddamar da sabbin rumfuna rajistar katin zabe amma mutane da dama basu fito yin rajista ba.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/7088527389cf07c9.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Bai Tsinana Mana Komai Ba: Matasa Da Mata Sun Huro Wuta A Karamar Hukuma, Sun Ce Dole A Tsige Ciyaman
![Legit NG Legit NG](https://cdn.legit.ng/images/1120/0239b82929c1665c.jpeg?v=1)
Asali: Depositphotos
Zarewa yace ,
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
“Bisa bincikin da suka yi a watan Mayu 2022 cikin rumfuna 1,750 da suka kaddamar, rumfuna 1,200 basu samu sama da mutane 50 da sukayi rajista a kowani rumfa ba.
“Duk da yake an samu matsalar yanke kafofin sadarwa a kananan hukumumi 17 daga cikin 34 na jihar na watanni biyar saboda matsalar harkar tsaro," Inji shi.
Ta tabbata: INEC ta amince da takarar gwamnan Kano ga dan janar Abacha a PDP
A wani labari - Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta tabbatar da cewa ta sa idon basira a zaben fidda gwani da ya samar da Mohammad Abacha a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Kano.
Kafin bayanin na INEC dai an yi ta cece-kuce kan wanda hukumar za ta amince da shi a matsayin dan takarar gwamna tsakanin Mohammed Abacha da Sadiq Wali.
Asali: Legit.ng