Yanzu-Yanzu: Dan takarar gwamna ya janye daga takara, ya fice daga jam'iyyar APC

Yanzu-Yanzu: Dan takarar gwamna ya janye daga takara, ya fice daga jam'iyyar APC

  • Na gaba-gaba a takarar gwamnan jihar Rivers a APC ya sauya sheka a daidai lokacin da ake shirin fara zaben fidda gwani
  • Wannan na zuwa ne bayan zargin da dan takarar ya yi na cewa, akwai makarkashiya a tafiyar da tsarin jam'iyyar
  • Hakazalika, ya kira masoyansa da su kula, kuma kada su bata lokaci wajen halartar zaben da aka shirya manakisa

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Rivers - Sanata Magnus Abe ya fice daga jam’iyyar APC mai mulkin kasar nan. Ya kuma fice daga takarar Gwamna a APC a jiharsa.

The Nation ta ruwaito cewa, Abe ya bayyana janyewarsa daga takara ne ta hannun kodinetan kungiyar kamfen na Bola Ahmed Tinubu Support Vanguard (BATS-V), Sir Tony Okocha na Kudu maso Kudu.

Dan takarar APC ya fice daga takarar gwamnan jihar Rivers
Yanzu-Yanzu: Dan takarar gwamna ya janye takara, ya fice daga jam'iyyar APC | Hoto: thenationonlineng.net
Asali: Depositphotos

Okocha ya ce duk da ficewa daga jam'iyyar APC, burin zama gwamnan jihar Rivers na Abe na nan daram.

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Bayan janyewa daga takarar shugaban kasa, Peter Obi ya fice daga PDP

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, sanarwar ta ce:

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

“Ina ta samun dimbin kiraye-kiraye daga abokan aikinmu game da zaben fidda gwani na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyarmu ta APC.
“Don Allah a dauki wannan a matsayin sanarwa a hukumance cewa ba za mu shiga gurbatacce tsari, na son zuciya, da son kai ba a RIVERS.
“Ana shawartar dukkan masu goyon bayan mu da kada su bata lokacinsu a cikin tsarin da ba zai haifar da da mai ido ba."

2023: Dasuki ya samu takarar Majalisa a PDP, yana goyon bayan Tambuwal a kan Atiku

A wani labarin, Hon. Abdussamad Dasuki shi ne wanda ya yi nasarar zama ‘dan takarar PDP na yankin Kebbe da Tambuwal a majalisar tarayya a zaben 2023.

This Day ta ce tsohon kwamishinan kudin ya samu babbar nasara a zaben tsaida gwanin da jam’iyyar PDP ta shirya a ranar 22 ga watan Mayu, 2022.

Kara karanta wannan

Rikicin PDP: Tashin hankali yayin da PDP ta dage zaben fidda gwani bayan barkewar rikici

Abdussamad Dasuki ya lashe duka kuri’u 65 da ‘ya ‘yan jam’iyyar PDP suka kada a zaben tsaida gwanin da aka gudanar kamar yadda sakamako ya nuna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.