Yanzu Yanzu: Kotu ta tabbatar da Sanata Adeleke a matsayin dan takarar gwamna na PDP a Osun

Yanzu Yanzu: Kotu ta tabbatar da Sanata Adeleke a matsayin dan takarar gwamna na PDP a Osun

  • Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Osogbo ta tabbatar da Sanata Ademola Adeleke a matsayin sahihin dan takarar jam’iyyar PDP a zaben gwamnan jihar Osun
  • Mai shari'a Nathaniel Emmanuel, ya kuma yi watsi da karar da Prince Dotun Babayemi ya shigar na neman a bayyana shi a matsayin dan takarar jam'iyyar adawar a zaben
  • Rahotanni sun nuna cewa za a dai gudanar da zaben gwamnan na jihar Osun ne a ranar 16 ga watan Yulin 2022

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Osun - Alkalin babbar kotun tarayya da ke zama a Osogbo, Justis Nathaniel Emmanuel, ya tabbatar da Sanata Ademola Adeleke a matsayin dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a zaben gwamnan Osun da za a yi a ranar 16 ga watan Yulin 2022, Channels TV ta rahoto.

Kara karanta wannan

Shugaban kasa a 2023: Ni nafi cancanta na gaji Buhari, in ji Saraki

Alkalin ya yi watsi da karar da Prince Dotun Babayemi ya shigar, inda yake neman a ayyana shi a matsayin dan takarar babbar jam’iyyar adawa ta kasar.

Yanzu Yanzu: Kotu ta tabbatar da Sanata Adeleke a matsayin dan takarar gwamna na PDP a Osun
Yanzu Yanzu: Kotu ta tabbatar da Sanata Adeleke a matsayin dan takarar gwamna na PDP a Osun Hoto: bbc.com
Asali: Facebook

Ya kuma soke zaben fidda gwanin da ya samar da Babayemi, wanda aka gudanar a cibiyar taro ta WOCDIF, Osogbo a ranar 8 ga watan Maris, 2022.

Har wayau, Justis Emmanuel ya ayyana cewa Sanata Ademola Adeleke ne sahihin zababben dan takarar PDP a zaben, rahoton The Nation.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Magudi akayi min a 2019, ni na lashe zabe: Atiku Abubakar

A wani labari na daban, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma mai neman kujeran shugaba a 2023 karkashin jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), ya jaddada cewa shi ya kashe zaben shugaban kasa a 2019.

Atiku yace kawai jam'iyyar All Progressives Congress (APC) ta yi amfani da karfin mulki wajen kwace nasarar daga hannunsa.

Kara karanta wannan

2023: Saura kwana 10 zabe, an shiga yamutsi a PDP game da wanda za a tsaida takara

Ya kara da cewa sam ba zasu taba yarda a sake musu irin wannan a zaben 2023 idan jam'iyyar PDP ta bashi tikiti.

Asali: Legit.ng

Online view pixel