Magudi akayi min a 2019, ni na lashe zabe: Atiku Abubakar

Magudi akayi min a 2019, ni na lashe zabe: Atiku Abubakar

  • Alhaji Atiku Abubakar ya ce wannan karon ba zai yarda a yi masa magudi kamar yadda akayi masa a 2019 ba
  • Shahrarren dan siyasan yace jam'iyya mai mulki ta yi amfani da karfin ofis wajen kwace nasara hannunsa
  • Jam'iyyar PDP ta dage ranar gudanar da zaben tsayar da gwanin dan takarar shugaban kasa

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Kaduna - Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma mai neman kujeran shugaba a 2023 karkashin jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), ya jaddada cewa shi ya lashe zaben shugaban kasa a 2019.

Atiku yace kawai jam'iyyar All Progressives Congress (APC) ta yi amfani da karfin mulki wajen kwace nasarar daga hannunsa.

Ya kara da cewa sam ba zasu taba yarda a sake musu irin wannan a zaben 2023 idan jam'iyyar PDP ta bashi tikiti.

Kara karanta wannan

Ba Ni Da Kuɗi Amma Ina Tausayin Ƴan Najeriya, Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a APC, Fayemi

Magudi akayi min a 2019, ni na lashe zabe: Atiku Abubakar
Magudi akayi min a 2019, ni na lashe zabe: Atiku Abubakar
Asali: Getty Images

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Atiku ya bayyana hakan yayinda ya hadu da deleget din jihar Kaduna a sakatariyar jam'iyyar da daren Talata, rahoton Leadership.

Ya bukaci deleget din Kaduna su kada masa kuri'a kamar yadda suka yi a zaben 2018, ya yi alkawarin ba zai basu kunya ba.

Ya tabbatar musu da cewa ba karamin taimakawa Najeriya zai yi ba idan ya zama shugaban kasa.

Yace:

"Ni na lashe zaben 2019 amma aka yi min magudi, kamar yadda aka muku magudi a Kaduna ta hanyar amfani da karfin mulki, amma ba zamu bari hakan ya sake faruwa ba a 2023."
"Saboda haka ina kira ga ku zabi shugabannin kwarai, idan na samu tikitin jam'iyyar kuma na samu nasara a 2023, zan hada kan yan Najeriya."

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Sanata Ahmed Makarfi, a nashi jawabin yace lallai su suka lashe zabe a 2019 amma aka hanasu.

Kara karanta wannan

Manjo Hamza Al-Mustapha: Ina gaje Buhari zan tare a dajin Sambisa saboda dalilai

Atiku ya lissafa jihohi 5 da yake zargin APC ta sace masa kuri’u a 2019

Legit Hausa ta zakulo jerin jihohi biyar da dan siyasar wanda ya kasance haifaffen jihar Adamawa ya zargi APC da sace masa kuri’u, ga su kamar haka:

1. Jihar Katsina

2. Jihar Kano

3. Jihar Kaduna

4. Jihar Borno

5. Jihar Yobe

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng