APC, PDP, SDP: Farashin fom din takara a manyan jam'iyyun siyasa a Najeriya

APC, PDP, SDP: Farashin fom din takara a manyan jam'iyyun siyasa a Najeriya

Gabanin zaben 2023, yawancin jam’iyyun siyasa sun kayyade farashin tsayawa takara da kudin fom dinsu, lamarin da ya girgiza 'yan Najeriya da dama.

A cikin wannan labarin, Legit.ng Hausa ta jero kudaden da ake kashewa wajen sayen fom din takara a kujeru daban-daban ga mai son tsayawa takara a Najeriya a zabe mai zuwa, kamar yadda TheCable ta tattaro.

Farashin fom din takara a manyan jam'iyyun Najeriya
APC, PDP, SDP: Farashin fom a manyan jam'iyyun siyasa a Najeriya
Asali: Original

Ga su kamar haka:

PDP

  1. Shugaban kasa - N40m
  2. Gwamna - N21m
  3. Majalisar Dattawa - N3.5m
  4. Majalisar Wakilai ta kasa - N2.5m
  5. Majalisar jiha - N600k

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

APC

  1. Shugaban kasa - N100m
  2. Gwamna - N50m
  3. Majalisar Dattawa - N20m
  4. Majalisar Wakilai ta kasa - N10m
  5. Majalisar jiha - N2m

Kara karanta wannan

PDP ta ci kasuwa da kudin saida fam, ta tashi da N600m daga hannun ‘Yan takara 17

SDP

Shugaban kasa - N35m

Gwamna - N16m

Majalisar Dattawa - N3m

Majalisar Wakilai ta kasa - N1.7m

Majalisar jiha - N500k

Abin lura: Farashin na iya sauyawa a kowane lokaci, don haka za mu sabunta wannan jeri yayin da muka samu karin bayani.

Kofar rashawa: 'Yan Najeriya sun kadu da jin farashin fom din takarar shugaban kasa N100m a APC

A wani labarin, a jiya ne jam'iyyar APC ta yi zamanta gabanin zaben fidda gwani na 'yan takara a shirin zaben 2023 mai zuwa.

A taron ne jam'iyyar ta bayyana cewa, N100m za ta sayar da fom din takarar shugaban kasa yayin da ta ce a cikin kudi N30m na takarar ayyana niyya ne, N70m kuma kudin takardar neman kujeran ne.

Wannan lamari ya sanya 'yan Najeriya da dama cikin rudani, har ta jau ga da dama suka tofa albarkacin bakinsu game da wannar manufa ta jam'iyyar mai ci a yanzu.

Kara karanta wannan

An samu ‘Yan siyasa 2 da suka saye fam a PDP, za su jarraba sa’a kan Zulum a 2023

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.