‘A Ido na Yake Lalata da Mata’: Jarumar Fina Finai Ta Koka kan Halin Mijinta

‘A Ido na Yake Lalata da Mata’: Jarumar Fina Finai Ta Koka kan Halin Mijinta

  • Fitacciyar jarumar Nollywood, Mama Ereko, ta bayyana wahalhalun da ta sha a aurenta, ta ce mijinta na kawo mata mata gida a gabanta
  • Ta bayyana cewa ta yanke shawarar kin yin aure bayan mutuwar mijinta inda ta fi mayar da hankali kan 'ya'yanta da kiyaye kyan fatarta
  • Mama Ereko ta ce ta sha wahala a masana'antar fim, inda masu sayar da fina-finai suka hana ta riba har sai da ta hadu da AbdulRazaq
  • Ta ce bata fuskanci cin hanci don samun rawa a fina-finai ba, ta kuma shawarci matasa su fara yin fina-finai da kansu ba tare da bata lokaci ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ikeja, Lagos - Fitacciyar jarumar Nollywood, Morenike Sulaimon, wacce aka fi sani da Mama Ereko, ta bayyana wahalhalun da ta fuskanta a aurenta da mijinta marigayi.

Kara karanta wannan

Alamar rauni ne: Tsohuwar Sanata ta dura kan Natasha game da zargin Akpabio

Mama Ereko ta fara fim a 1982, amma ta dakata kafin ta dawo a 1994, tun daga lokacin, ta fito a fina-finai da dama, ciki har da Ebun da Ajulo.

Jarumar fim ta koka yadda mijinta ke cin amanarta
Jarumar fim, Mama Ereko ta fadi yadda mijinta ke lalata da mata a gabanta. Hoto: Yoruba Celebrities.
Asali: Facebook

Jarumar fim ta fadi matsalolin aurenta

A wata hira da aka wallafa a YouTube, jarumar mai shekaru 79 ta ce 'ya'yanta suna kanana lokacin da mahaifinsu ya rasu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jarumar ta ce ta sha wahala sosai a rayuwar aurenta wanda mijinta ke zuwa da mata har cikoin gidanta.

Mama Ereko ta ce:

“Ya kan aikeni yawon hidima idan yana shirin kawo wata mace, Idan na dawo, sai in tarar da wata a gida, amma na gode wa Allah.”
"Dayar budurwar tasa ta fi tsaurin ido, Har tana kwana a gidana, Nakan ji haushi, amma ban isa in ce komai ba, saboda tsoron mijina."
Jaruma ta fallasa yadda mijinta ya ci amanarta
Jarumar fim, Mama Ereko ta fadi dalilinta na kin sake aure. Hoto: @officialmamaereko.
Asali: Instagram

Dalilin jaruma Ereko na kin yin aure

Bayan mutuwar mijinta, Mama Ereko ta ce ta yanke shawarar kin yin aure, domin ta fi son kula da ’ya’yanta da kuma lafiyarta.

Kara karanta wannan

Bauchi: Miji ya yi wa matarsa dukan tsiya har ta zarce lahira kan abincin Ramadan

“Idan na sake aure, da ba za ku yaba min ba, Kuma damuwar aure da jima’i na sa mace ta tsufa fiye da shekarunta.”
“Ban ma san yadda jin dadin namiji yake ba, Babu bukatar sake aure a rayuwata.”

Ta kuma yi bayani kan wahalhalun masana’antar fim, inda ta ce ta yi fina-finai goma ba tare da samun riba ba har sai da ta hadu da AbdulRazaq.

"Na sha wahala a masana'antar nan, Masu siyar da fim sun hana ni riba, amma AbdulRazaq ne ya ceci rayuwata, ya ba ni shawarwari masu amfani."

Game da cin hanci don samun rawa a fina-finai, ta ce babu wanda ya taba nemanta don haka inda ta shawarci matasan 'yan fim da su fara shirya nasu fina-finai ba tare da bata lokaci ba.

Hadiza Gabon ta caccaki masu sukarta

Kun ji cewa jarumar Hadiza Aliyu Gabon ta bayyana cewa duk wanda ya zage ta ko ya ɗauki alhakinta ba ta yafe ba duk da an shigo watan azumi.

Kalaman fitacciyar jarumar sun ja hankalin mabiyanta, wasu na ganin hakan bai dace ba kwata-kwata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

iiq_pixel