Tinubu Zai Ziyarci Jihohi 4, Zai Fara da Jos inda Aka Kashe Musulmai da Kiristoci
- Shugaba Bola Tinubu ya dage ziyarar jihar Ogun ta gobe Laraba domin ya ziyarci birnin Jos don jajantawa mutanen da hare-hare suka shafa
- Bayan ziyarar Plateau, shugaban zai wuce birnin Legas domin gudanar da bukukuwan Good Friday da Easter tare da kaddamar da ayyuka
- A ranar 4 ga watan Afrilu, shugaban kasar zai kaddamar da filin jirgin sama na Gateway dake jihar Ogun domin bunkasa tattalin arzikin kasa
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Fadar shugaban ƙasa ta sanar da cewa Shugaba Bola Tinubu ya sauya fasalin ziyarar da ya shirya kai wa jihohi huɗu na ƙasar nan tun daga yau Laraba, 1 ga Afrilu, 2026.
Maimakon tafiya garin Iperu dake jihar Ogun gobe kamar yadda aka tsara, shugaban zai garzaya Jos, babban birnin jihar Plateau, domin jajantawa gwamnati da al'umma kan hare-haren 'yan bindiga na baya-bayan nan da suka lakume rayukan bayin Allah.

Source: Twitter
Tinubu zai ziyarci Jos, Legas, Ogun
Mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ne ya bayyana sabon jadawalin tafiye-tafiyen Tinubu a cikin sanarwar da ya fitar a shafinsa na X.
Bayan kammala ziyarar ta'aziyya a Plateau, Shugaba Tinubu zai wuce birnin Legas domin gudanar da bukukuwan Good Friday.
A ranar Asabar, 4 ga watan Afrilu, shugaban zai koma jihar Ogun domin kaddamar da Filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa na Gateway International Cargo Airport.
Hakazalika, zai kaddamar da jiragen kasuwanci guda biyu da za su rinka safarar kayayyaki zuwa ƙasashen waje da kuma sabon babban ofishin rundunar kwastam ta tarayya (FOU) da kuma motocin sintiri na zamani.
Tinubu zai kaddamar da ayyuka a Legas
Yayin da yake ci gaba da hutun Easter a Legas, shugaban zai kaddamar da wasu muhimman ayyukan more rayuwa da gwamnatin Gwamna Babajide Sanwo-Olu ta kammala.
Waɗannan sun haɗa da:
- Gagarumar gadar nan ta Ojota/Opebi Link Bridge.
- Katafaren ginin nan na cibiyar bayanan yanayin kasa ta Legas (GIS).
- Wani katafaren ginin hukumomi da aka sanya wa sunan shugaban ƙasar kansa.

Source: Twitter
Ziyara zuwa jihar Bayelsa
Kafin ya koma fadar shugaban ƙasa dake Abuja, Shugaba Tinubu zai kai ziyara jihar Bayelsa a ranar 10 ga watan Afrilu, kamar yadda sanarwar Onanuga ta nuna.
Shugaba Tinubu zai kai ziyarar ne domin taya Gwamna Duoye Diri kaddamar da wasu daga cikin manyan ayyukan da ya kammala a jiharsa.
Wannan ziyarce ziyarce na kwanaki 10 yana nuna yunƙurin gwamnatin tarayya na ƙarfafa haɗin kai tsakanin jihohi da kuma nuna kulawa ga matsalolin tsaro da na tattalin arziƙi a lokaci guda.
'An kashe Musulmai 4 a Jos' - JNI
A wani labari, mun ruwaito cewa, kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) ta bayyana adadin Musulman da aka kashe a wani hari da aka kai a Filato.

Kara karanta wannan
Tinubu ya shirya karbo bashin sama da Naira tiriliyan 8, ya tura sako Majalisar Dattawa
Hakan na zuwa ne bayan wasu 'yan ta'dda sun kai harin mai uwa da wabi kan jama'a da dare a jihar Filato, inda sama da mutum 20 suka mutu.
A yanzu haka dai kungiyar JNI ta sanar da cewa akalla Musulmai 10 ne ba a san a ina suke ba tun bayan harin da aka kai kuma ana neman su.
Asali: Legit.ng

