Diflomasiyya: Jerin kasashe 10 da suka amince da naɗin sabbin jakadun Najeriya
- Ma'aikatar harkokin waje ta ce ƙasashe 10 sun aiko da takardun amincewa da sababbin jakadun Najeriya da aka tura musu
- Daga cikin jakadun da aka amince da su har da tsohon shugaban INEC Mahmud Yakubu da kuma tsofaffin shugabannin hukumomin tsaro
- Har yanzu ana jiran martani daga Jamus da Mexico kan naɗin Femi Fani-Kayode da Reno Omokri a matsayin jakadun Najeriya a can
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta sanar da cewa ta karɓi takardu daga ƙasashe guda 10 da suka amince da naɗin sababbin jakadun da Shugaba Bola Tinubu ya tura masu.
Kakakin ma'aikatar, Kimibie Ebienfa, ya bayyana cewa ƙasashen da suka amince a nade-naden sun haɗa da Birtaniya, Faransa, Amurka, Ireland, Qatar, Jamhuriyar Benin, Habasha, Djibouti, Senegal da Saliyo.

Kara karanta wannan
Mojtaba Khamenei: Daga karshe an bayyana kasar da sabon jagoran addini na Iran yake

Source: Twitter
Kasashe 10 sun amince da jakadun Najeriya
Jaridar The Cable ta ruwaito Ebienfa, a cikin sanarwar da ya fitar, ya bayyana cewa:
"Ina son sanar da ku cewa har yanzu muna ci gaba da karɓar saƙonnin amincewa daga ƙasashen da aka tura jakadunmu zuwa gare su."
Daga cikin sunayen da ƙasashen suka amince da su, akwai tsofaffin shugabannin hukumomin tsaro da kuma ƙwararrun ma'aikatan diflomasiyya waɗanda aka ba wa muƙaman.
Aminu Dalhatu ne zai wakilci Najeriya a Birtaniya, yayin da tsohon shugaban DSS, Kayode Are, zai ƙasar Amurka. Shi kuwa tsohon shugaban hukumar NIA, Ayodele Oke zai yi aiki a ƙasar Faransa.
Haka kuma, an tabbatar da karbar tsohon shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC), Farfesa Mahmud Yakubu, a matsayin jakadan Najeriya a ƙasar Qatar.
Jiran martani kan Fani-Kayode da Omokri
Duk da samun amincewar waɗannan jakadu 10, sanarwar ta nuna cewa har yanzu ana jiran martani daga ƙasar Jamus inda aka tura Femi Fani-Kayode, da kuma ƙasar Mexico inda aka tura Reno Omokri.
Ma'aikatar ta bayyana cewa:
"Ana sa ran samun saƙon amincewa ga Femi Fani-Kayode da aka tura Jamus, da kuma Reno Omokri wanda aka tura ƙasar Mexico nan ba da daɗewa ba."
Masana diflomasiyya sun bayyana cewa wannan tsari na jiran amincewar ƙasashe abu ne na yau da kullum dake ɗaukar lokaci kafin kowace ƙasa ta tantance wanda aka tura mata, in ji rahoton Punch.

Source: Twitter
Shirye-shiryen rantsar da da jakadun
Shugaba Tinubu ya riga ya amince da tura ƙwararrun jakadu 31 da kuma wadanda ba ƙwararru ba 34 zuwa ƙasashe daban-daban da kuma Majalisar Ɗinkin Duniya.
Ma'aikatar ta tabbatar da cewa za a sanar da ranar gudanar da taron rantsar da sababbin jakadun da kuma ba su horo da zarar fadar shugaban ƙasa ta kammala shirye-shiryenta.
Tun a watan Satumban 2023 ne shugaban ƙasar ya dawo da dukkan jakadun Najeriya dake ƙasashen waje gida, inda ya fara naɗa sababbi tun a watan Nuwamban 2025.
Kasashe sun ki karbar jakadun Najeriya
A wani labari, mun ruwaito cewa, Indiya da wasu kasashe sun ki amincewa da wasu daga cikin jakadun da Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada kwanan nan.
Wasu manyan jami’ai a fadar shugaban kasa da kuma ma’aikatar harkokin waje sun bayyana cewa Indiya, tana da wata doka da ta dade tana bi wadda ke hana karbar jakadu.
Wasu majiyoyi sun ce gwamnatin tarayya ta riga ta fara samun sakonni daga New Delhi da ma wasu manyan kasashe cewa ba su da niyyar karbar jakadu.
Asali: Legit.ng

