El Rufai Zai Ci Gaba da Zama a hannun ICPC duk da Rasuwar Mahaifiyarsa
- Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai na ci gaba da jimamin rasuwar mahaifiyarsa wadda ta riga mu gidan gaskiya a makon jiya
- Ana cikin zaman makokin Hajiya Umma El-Rufai, tsohon gwamnan ya bayyana a gaban kotu domin ci gaba da shari'a kan tuhume-tuhumen da ICPC ke yi masa
- Hakazalika, El-Rufai zai ci gaba da zama a tsare a hannun hukumar ICPC har zuwa lokacin da kotu za ta yi hukunci kan bukatar neman belin da ya gabatar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Kaduna - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, zai ci gaba da zama a hannun hukumar ICPC.
An mayar da Malam Nasir El-Rufai, hannun hukumar yaƙi da cin hanci da sauran laifuffuka masu alaƙa da hakan (ICPC).

Source: Facebook
Jaridar Daily Trust ta kawo rahoton cewa an mayar da El-Rufai hannun hukumar ICPC ne a ranar Talata, 31 ga watan Maris 2026.
Naisr El-Rufai ya sake bayyana gaban kotu
Tsohon gwamnan, wanda ya bar hannun ICPC a ranar 27 ga Maris, 2026, biyo bayan rasuwar mahaifiyarsa, an sake gurfanar da shi a farkon ranar Talata.
Kafin nan, kotun ta ɗage saurarar buƙatarsa ta neman belin zuwa ranar 31 ga Maris, 2026.
Amma, a ranar Talata, ya fara bayyana ne a babbar kotun jihar Kaduna kan wata tuhuma ta daban da hukumar ICPC ta shigar kansa.
Rashin halartar wanda ake ƙara na biyu ya dakatar da saurarar ƙarar, inda aka ɗage ta zuwa ranar 10 ga Afrilu, 2026.
Bayan haka, aka tafi da shi zuwa babbar Kotun rarayya da ke Kaduna, wadda aka tsara za ta saurari buƙatarsa ta neman beli.
Jami'an ICPC sun yi wa El-Rufai rakiya
Jim kaɗan bayan tashi daga zaman kotun, jami’an hukumar yaƙi da cin hanci da sauran laifuffuka masu alaƙa (ICPC) sun raka El-Rufai fita daga harabar kotun a cikin wata farar mota ƙirar Hilux.
Kafin nan, tsohon gwamnan ya koma kotun ne a cikin tsauraran matakan tsaro domin ci gaba da sauraren buƙatarsa ta neman beli.
Bayan kammala zama a babbar kotun jiha, hukumar ta mayar da El-Rufai zuwa babbar kotun Tarayya da ke cikin haraba guda domin ci gaba da sauraron shari’ar.

Source: Facebook
El-Rufai ya koma hannun ICPC
Sakamakon ɗage zaman da aka yi, ana sa ran a Laraba za a ci gaba da sauraron buƙatar tasa ta neman beli.
Bayan bayyanar tasa a kotu, an mayar da shi hannun hukumar ICPC yayin da ake ci gaba da gudanar da shari’o’in da ake yi kansa, rahoton Vanguard ya tabbatar da hakan.
El-Rufai ya sauke Kur'ani a hannun ICPC
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ya yi amfani da lokacin da aka tsare shi a hannun ICPC ta hanya mai kyau.
Wani makusancin El-Rufai ya bayyana cewa tsohon gwamnan bai yi asarar lokaci ba, domin ya yi amfani da lokacin da ya kwashe a tsare wajen ibada da karatu mai zurfi.
Ya kara da cewa El-Rufai ya kammala karatun Alƙur’ani mai tsarki gaba ɗaya, ya karanta littattafai guda 10, sannan ya rubuta wasu littattafai a lokacin da yake tsare.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

