NiMet: Gombe, Bauchi da Jihohin da za Sha Ruwan Sama a Arewa a Yau Litinin
- Hukumar hasashen yanayi ta kasa (NiMet) ta fitar da hasashen yadda yanayi zai kasance a yau Litinin, 30 ga watan Maris, 2026 a jihohi
- NiMet ta sanar da cewa za a wayi gari da rana a wasu jihohin Arewacin Najeriya, yayin da za a samu ruwan sama da yamma a wasu
- Domin kare rayuka da dukiyoyin jama'a, hukumar ta sanar da matakan da ya kamata kowane mutum ya dauka a yankunan Najeriya
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Gombe - Rahoton hasashen yanayi da hukumar NiMet ta fitar na yau Litinin, 30 ga watan Maris 2026 ya nuna cewa za a samu ruwan sama a wasu jihohi.
Hakan na zuwa ne yayin da damuna ta fara dawowa a wasu jihohin Arewacin Najeriya, inda aka samu ruwan sama a wasu yankuna.

Source: Facebook
A sakon da NiMet ta wallafa a shafinta na X, Legit Hausa ta gano cewa jihar Gombe na cikin jihohin da ake hasashen samun ruwan sama a yau.
Jihohin Arewa da za a yi ruwa
Hasashen NiMet ya nuna cewa ana sa ran yanayi mai dauke da hasken rana tare da ɗan gajimare a yankunan Arewacin Najeriya da safe.
Daga rana ta daga zuwa yamma, ana sa ran tsawa tare da ruwan sama matsakaici a jihohin Taraba, Kudancin Kebbi, Kudancin Adamawa, Kudancin Zamfara, Kudancin Katsina, Gombe da Bauchi.
Hasashe a wasu jihohin Arewa
A wasu jihohin Arewa ta Tsakiya, rahoton ya nuna cewa za a tashi da zafi da safe sannan a samu tsawa daga baya, inda ake sa ran samun gajimare a yankin.
Hukumar NiMet ta ce ana iya samun tsawa a wasu wurare tare da ruwan sama matsakaici a jihohin Kwara, Niger da Kogi a yau.
Za a yi ruwa a jihohin Kudu
Hasashen yanayi ya nuna cewa za a samu gajimare tare da hasken rana kadan lokaci bayan lokaci da safe a Kudancin Najeriya.
Daga baya kuma, rahoton ya ce ana iya samun tsawa tare da ruwan sama matsakaici a jihohin Delta, Edo, Cross River, Akwa Ibom
NiMet ta bayyana cewa hasashen ya nuna cewa ana sa ran tsawa tare da ruwan sama matsakaici a duk faɗin yankin da yamma.
Gargadin NiMet ga jama'a
Saboda iska mai ƙarfi na iya fara zuwa kafin tsawa a jihohi, NiMet ta bukaci al'umma su gyara abubuwan da iska za ta iya ɗauka.

Source: Getty Images
Yayin da aka samu ruwan sama, hukumar ta bukaci a rika tuki a hankali saboda kaucewa zamewa a hanyoyi a lokacin da ake tafiya da babur da sauransu.
Hukumar ta bukaci a cire na’urorin lantarki domin kauce wa lalacewa sakamakon walƙiya, sannan a sha ruwa sosai, musamman a yankunan da ake hasashen samun rana.
NiMet ta ce za a yi ruwan sama
A wani labarin, mun kawo muku hasashen da hukumar NiMet ta yi game da yadda yanayi ya kasance a ranar Juma'a, 27 ga watan Maris, 2026.
A jihohin Arewa, hukumar ta sanar da cewa akwai alamun samun ruwa da yamma a jihohin Sokoto, Kebbi bayan an yi rana da safe.
A Kudancin Najeriya kuma, NiMet ta sanar da cewa za a samu ruwa mai yawa a jihohin da suka hada da Legas, Rivers da Bayelsa.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


