"Muna cikin Babbar Matsala," Baba Ahmed Ya Cire Tsoro, Ya Yi wa Tinubu Kaca Kaca

"Muna cikin Babbar Matsala," Baba Ahmed Ya Cire Tsoro, Ya Yi wa Tinubu Kaca Kaca

  • Hakeem Baba-Ahmed ya bayyana cewa Najeriya tana cikin mawuyacin hali fiye da yadda Shugaba Bola Tinubu ya same ta a shekarar 2023
  • Tsohon mai ba shugaban shawara ya koka kan yadda Tinubu ya jagoranci zugar ministoci suka tafi shagali a Birtaniya bayan an kashe mutane a Borno
  • Baba-Ahmed ya jaddada cewa shugaba Tinubu ya gaza cika alkawuran da ya dauka na samar da tsaro da inganta rayuwar 'yan Najeriya

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Tsohon mai ba Shugaba Bola Tinubu shawara na musamman kan lamuran siyasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya yi tsokaci game da yadda lamura ke tafiya a Najeriya a halin yanzu.

Hakeem Baba-ahmed ya bayyana cewa mawuyacin halin da Najeriya take ciki a yanzu ya rubanya fiye da lokacin da Tinubu ya karɓi mulki a shekarar 2023.

Kara karanta wannan

Faransa za ta bi sahun Amurka, za a kawo wa Najeriya agaji a kan rashin tsaro

Hakeem Baba Ahmed ya ce Tinubu ya jefa Najeriya a mawuyacin hali fiye da yadda ya same ta a 2023.
Tsohon hadimin shugaban kasa, Hakeem Baba Ahmed (hagu) da Shugaba Bola Tinubu (dama). Hoto: Hakeem Baba-Ahmed, Bayo Onanuga.
Source: Facebook

Halin da Najeriya take ciki karkashin Tinubu

Tsohon hadimin Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin wata hira da gidan talabijin na Trust TV, inda ya koka kan yadda matsalar tsaro da tattalin arziki ke neman fin karfin gwamnati.

A cewar Baba-Ahmed, ko shi kansa shugaban ƙasar ya san cewa bai cika alkawuran da ya ɗauka wa ‘yan ƙasa ba. Ya bayyana cewa:

“Muna cikin matsala mai zurfi fiye da lokacin da ka zo. Tasu-tasun hankali sun daɗa tsananta fiye da yadda muke tsammani.”

Ya ƙara da cewa shekaru uku bayan fara mulkin Tinubu, ana fuskantar wani salo na tashin hankali da zubar da jini waɗanda ba a taɓa ganin irinsu ba a tarihin ƙasar.

Baba-Ahmed ya soki Tinubu kan zuwa Birtaniya

Baba-Ahmed ya nuna bacin ransa game da yadda shugaban ƙasa ya jagoranci ayarin ministoci da jami’an gwamnati zuwa ƙasar Birtaniya a wata ziyarar ban-girma, a daidai lokacin da al’umma ke cikin makoki.

Kara karanta wannan

Zai shiga APC ne? Sule Lamido ya bude kofar ganawa da Shugaba Bola Tinubu

Ya ce:

“Kwanaki kaɗan da suka gabata, shugaban ƙasa da babban ayarin ministoci sun tafi Birtaniya. Ziyarar ta kasance ta shagali da jin daɗi, a cewar rahotannin kafafen yaɗa labarai.”

Ya yi nuni da cewa wannan shagalin ya faru ne ‘yan kwanaki kaɗan bayan an kai wasu munanan hare-hare a jihar Borno waɗanda suka yi sanadiyyar asarar rayuka.

Hakeem Baba-Ahmed ya ce:

“Shugaban ƙasa da kansa zai amince cewa ya gaza, watau ya gaza cika alkawuran da ya yi, ya gaza samar da tsaro ga ‘yan Najeriya.”
Hakeem Baba Ahmed ya ce Tinubu ya gaza cika alkawuran da ya daukar wa 'yan Najeriya
Shugaba Bola Ahmed Tinubu a dakin taron TICAD 9 da aka gudanar a Japan. Hoto: @officialABAT
Source: Twitter

Alkawuran da Tinubu bai cika ba

Tsohon mai ba shugaban shawarar ya tuna wa ‘yan Najeriya cewa Tinubu ya hau mulki ne da alkawarin kawo ƙarshen rashin tsaro da kuma samar da sabuwar hanyar jin daɗin rayuwa.

Sai dai a cewarsa, maimakon haka, rayuwa ta ƙara yin tsada, sannan an samu karin yaduwar tashe tashen hankula a sassan ƙasar.

Wannan bayani na Baba-Ahmed, wanda ya kasance a cikin gwamnatin a baya, ya sake rura wutar muhawara kan irin nasarorin da gwamnatin Tinubu ta samu ko kuma gazawarta a fannin kare rayuka da dukiyoyin al'umma bayan shafe kusan shekaru uku a kan mulki.

Kara karanta wannan

Sheikh Mansur Sokoto ya yi wa Tinubu tsirara kan matsalolin Musulmi a Najeriya

Kalli hirar Baba Ahmed a nan kasa:

Baba-Ahmed ya yi gargadi kan tazarcen Tinubu

A wani labari, mun ruwaito cewa, tsohon hadimin shugaban kasa, Hakeem Baba-Ahmed ya yi tsokaci game da tazarcen shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.

A wata hira da aka yi da shi, Dr Baba-Ahmed ya yi hasashen cewa akwai hadari mai girma a idan shugaban ya samu damar yin wa'adi na biyu a 2027.

Ya bayyana haka ne inda ya ce har yanzu bai ga wani sauyi mai ma'ana da gwamnatin Bola Tinubu ta kawo ba tun bayan ajiye aiki da ita da ya yi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com