An Samu Matsala: Dangote Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Lita Ta Haura N1240

An Samu Matsala: Dangote Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Lita Ta Haura N1240

  • Matatar man Dangote ta kara farashin man fetur da take sayarwa abokan huldarta da ₦70, wanda ke nufin lita daya yanzu ta koma ₦1245
  • Sabon farashin zai fara aiki ne daga karfe 12:00 na daren yau Asabar, kuma zai shafi har da man da aka biya kudinsa amma ba a dauka ba
  • An dora alhakin wannan karin kudin a kan tashin hankalin da ake fama da shi a Gabas ta Tsakiya wanda ya shafi farashin danyen mai

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Legas - Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da abokan cinikinta cewa ta sauya farashin tataccen man fetur (PMS), inda aka samu ƙarin kuɗi yanzu.

A sakon da matatar ta aike wa abokan hulɗarta, ta sanar da su cewa ta ƙara farashin lita ɗaya daga ₦1,175 zuwa ₦1,245.

Kara karanta wannan

Bukukuwan Sallah: Jerin gwamnonin Arewa 5 da za su biya albashin Maris da wuri

Matatar man Dangote ta kara farashin litar man fetur da N70.
Hagu zuwa dama: Alhaji Aliko Dangote, shugaban rukunin kamfanonin Dangote, da wani ma'aikaci yana sayar da fetur. Hoto: Dangote Industries|Getty Images
Source: Getty Images

Dangote ya ƙara kuɗin man fetur

Wannan na nufin an samu ƙarin ₦70 a kan kowace lita ɗaya ta man fetur ɗin da ake saya daga matatar, kamar yadda Imran Muhammad ya wallafa a shafinsa na X.

Matatar Dangote ta ce wannan sabon farashi zai fara aiki ne daga ƙarfe 12:00 na daren yau, watau wayewar garin Asabar, 21 ga Maris, 2026.

Haka zalika, wannan ƙarin zai shafi dukkan man da aka riga aka biya kuɗinsa amma ba a ɗiba ba tukuna daga matatar.

Dalilin ƙarin kuɗin fetur

Baya ga ƙarin farashin lita, matatar ta kuma ƙara farashin samar da man ta hanyar ruwa daga ₦1,512,648 zuwa ₦1,606,518 a kan kowane tan ɗaya.

Matatar ta bayyana cewa ta ɗauki wannan matakin ne sakamakon rikice-rikicen da ke ci gaba da faruwa a matakin duniya, wanda ya shafi harkar makamashi gaba ɗaya.

Sharudan sayen fetur din Dangote

Matatar ta fayyace cewa abokan huldarta da ke da Bank Guarantees a turance, za su iya ci gaba da loda man su a ƙarƙashin tsarin da suke kai, muddin sun amince za su biya sauran ragowar kuɗin da aka ƙara a kai.

Kara karanta wannan

Kasashe 5 da za su iya shiga cikin yakin Amurka, Isra'ila da Iran

Hazalika, dole ne duk wani mai sayen mai da ake binsa ragowar kuɗin wannan ƙarin, ya kammala biya kafin ranar Litinin, 23 ga Maris, 2026, kamar yadda rahoton shafin Pulse ya nuna.

Wannan ƙarin na zuwa ne a daidai lokacin da farashin danyen mai ke ci gaba da tashi a kasuwannin duniya sakamakon rikicin da ake fafatawa a Gabas Ta Tsakiya tsakanin Iran da Amurka da Isra'ila.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com