Bayan Sanarwar Saudiyya, Sarkin Musulmi Ya Fadi Ranar da Za a Yi Karamar Sallah a Najeriya

Bayan Sanarwar Saudiyya, Sarkin Musulmi Ya Fadi Ranar da Za a Yi Karamar Sallah a Najeriya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto, Nigeria - Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar II, ya sanar da ranar da za a yi idin karamar Sallah a Najeriya.

Sarkin, wanda shi ne shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya ya ce ba a samu rahoton ganin jinjirin watan Shawwal, 1447AH ba a yau Laraba, 29 ga Ramadan.

Kara karanta wannan

29 ko 30: Malamin addini ya riga sarkin Musulmi, ya sanar da ranar karamar Sallah a Najeriya

Sarkin Musulmi.
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III Hoto: Daular Usmaniyya
Source: Facebook

Hakan na kunshe a wata sanarwa da shafin Daular Usmaniyya ya wallafa a Facebook mai dauke da sa hannun Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin harkokin addini na fadar Sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Wali Junaidu.

Ba a ga watan Sallah ba a Najeriya

Sanarwar ta bayyana cewa kwamitin ganin wata na fadar Sarkin Musulmi bai samu sahihin rahoton ganin wata daga ko'ina ba a fadin Najeriya.

Bisa ga wannan bayani, ranar Alhamis, 19 ga watan Maris, za ta zama ranar da za a cika azumi na 30 a watan Ramadan.

Sarkin Musulmin ya ayyana ranar Juma'a, 20 ga watan Maris, 2026 a matsayin ranar karamar Sallah, watau 1 ga watan Shawwal 1447AH.

Ya bukaci Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci na bikin Karamar Sallah wajen yin addu'o'in neman zaman lafiya, hadin kai, da dorewar ci gaba a Najeriya.

Sanarwar da Aarkin Musulmi ya fitar

Sanarwar ta ce:

Kara karanta wannan

Bayan gama duban jinjirin wata, kasar Saudiyya ta sanar da ranar karamar Sallah

"Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar CFR, mni, kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), ya karbi rahoton duban wata, wanda ya nuna ba a ga jinjirin wata ba a yau Laraba.
"Bisa haka, ya ayyana ranar Juma’a, 20 ga Maris, 2026, a matsayin 1 Shawwal 1447AH (Ranar Karamar Sallah). Ya kuma taya al'ummar Musulmin Najeriya murnar zagayowar wannan lokaci, sannan yana yi musu fatan samun shiriya da albarka.
"Ya kuma bukaci a ci gaba da addu'o'in neman zaman lafiya, ci gaba, da bunkasar kasar nan. Haka zalika, yana yi wa musulmi fatan alheri da shagalin Karamar Sallah lafiya. Allah (SWT) Ya karbi ayyukanmu na ibada, amin."
Sarkin Musulmi.
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III Hoto: Daular Usmaniyya
Source: Facebook

Ba a ga wata ba a Saudiyya

A dazu, kun ji cewa Saudiyya ta tabbatar da cewa ba a samu sahiihin rahoton ganin jinjirin watan Shawwal na shekarar 1447AH ba a yau Laraba, 29 ga watan Ramadan.

Bisa haka, masarautar Saudiyya ta bayyana cewa musulmi za su cika azumi 30 cif a wannan shekara, tare da ayyana ranar Juma'a, 20 ga watan Maris, 2026 a matsayin ranar karamar Sallah.

Hakan na kunshe ne a sanarwar da hukumar kula da masallacin Harami da Masallacin Annabi SAW, ta fitar bayan kammala tattara bayanai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262