Cikakken Jerin Sunaye da Kasashen da Tinubu Ya Tura Sababbin Jakadun Najeriya
Abuja - Shugaba Bola Tinubu ya amince da tura jakadu 65 wadanda aka nada zuwa kasashe daban-daban da kuma Majalisar Dinkin Duniya (UN) domin karfafa wakilcin Najeriya a kasashen waje.
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ne ya sanar da wannan mataki a ranar Alhamis, 6 ga watan Maris 2026.

Source: Twitter
Bola Tinubu ya tura jakadu zuwa kasashen waje
A sanarwar da ya wallafa a shafinsa na X, Onanuga ya ce jerin sunayen ya kunshi mutane 31 da ba ma'aikatan diflomasiyya ba (non-career) da kuma kwararrun ma'aikatan diflomasiyya (career diplomats) guda 34.
A cikin watan Nuwamban shekarar da ta gaba ne Shugaba Tinubu ya zaɓi waɗannan mutane, inda daga bisani Majalisar Dattawa ta tantance su tare da tabbatar da naɗin nasu a watan Disamba.
Ma'aikatar harkokin waje ta riga ta karɓi amincewar ƙasashe irin su Birtaniya don tura Jakada Aminu Dalhatu, da kuma ƙasar Faransa don tura Jakada Ayo Oke.
1. Jerin jakadu 31 (Non-Career)
Wannan rukunin ya ƙunshi fitattun ƴan siyasa da tsofaffin jami'an gwamnati:
S/N | Sunan jakada | Ƙasar da aka tura shi/ta |
1 | Grace Bent | Lome, Togo |
2 | Ita Enang | South Africa |
3 | Ikpeazu Victor | Spain |
4 | Nkechi Linda Ufochukwu | Tel-Aviv, Israel |
5 | Mahmood Yakubu | Qatar |
6 | Paul Oga Adikwu | Vatican City (Holy See) |
7 | Vice Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas | Philippines |
8 | Reno Omokri | Mexico City, Mexico |
9 | Abasi Ebraimah | Budapest, Hungary |
10 | Erelu Angela Adebayo | Portugal |
11 | Olumilua Oluwayimika Ayotunwa | Tokyo, Japan |
12 | Ugwuanyi Ifeanyi Lawrence | Athens, Greece |
13 | Chioma Priscilla Ohakim | Poland |
14 | Aminu Dalhatu | United Kingdom |
15 | Abdulrahman Bello Dambazau | Beijing, China |
16 | Tasiu Musa Maigari | Gambia |
17 | Olufemi Pedro | Australia |
18 | Muhammed Ubandoma Aliyu | Argentina |
19 | Lateef Kayode Are | United States of America |
20 | Joseph Sola Iji | Russia |
21 | Jimoh Ibrahim | UN Permanent Representative |
22 | Femi Fani-Kayode | Germany |
23 | Prof. Isaak Folorunsho Adewole | Ottawa, Canada |
24 | Fatima Florence Ajimobi | Austria |
25 | Lola Akande | Sweden |
26 | Ayodele Oke | France |
27 | Yakubu Gambo | Saudi Arabia |
28 | Prof. Nora Ladi Daduut | Seoul, South Korea |
29 | Onueze Chukwujika Okocha | Dublin, Ireland |
30 | Kulu Haruna Abubakar | Tunis, Tunisia |
31 | Jerry Samuel Manwe | Port of Spain, T&T |
2. Ƙwararrun ma'aikatan diflomasiyya
Ga jerin kwararrun ma'aikatan diflomasiyya 34 da aka tura su kasashe daban daban:
S/N | Sunan jakada | Ƙasar da aka tura shi/ta |
1 | Nwabiola Ezenwa Chukuwemeka | Cote D'Ivoire |
2 | Besto Maimuna Ibrahim | Niger |
3 | Monica Okwuchukwu Enebechi | Sao Tome, STP |
4 | Mohammed Mahmud Lele | Algiers, Algeria |
5 | Endoni Synoph Paebi | Ouagadougou, Burkina Faso |
6 | Ahmed Mohammed Monguno | Cairo, Egypt |
7 | Jane Adams | Kingston, Jamaica |
8 | Clark-Omeru Alexandra | Lusaka, Zambia |
9 | Chima Geoggrey David | Bamako, Mali |
10 | Odumah Yvonne Ehinosen | Malabo, E/Guinea |
11 | Wasa Segun Ige | Beirut, Lebanon |
12 | Ruben Abimbola Samuel | Rome, Italy |
13 | Onaga Ogechukwu Kingsley | Maputo, Mozambique |
14 | Magaji Umar | Kinshasa, DR Congo |
15 | Muhammed Saidu Dahiru | New Delhi, India |
16 | Abdulssalam Habu Zayyad | Dakar, Senegal |
17 | Shehu Ilu Barde | Accra, Ghana |
18 | Aminu Nasir | Ethiopia |
19 | Abubakar Musa Musa | N'Djamena, Chad |
20 | Haidara Mohammed Idris | The Hague, Netherlands |
21 | Bako Adamu Umar | Rabat, Morocco |
22 | Sulu-Gambari Olatunji Ahmed | Malaysia |
23 | Romata Mohammed Omobolanle | Tanzania |
24 | Shaga John Shamah | Botswana |
25 | Salau Hamza Mohammed | Tehran, Iran |
26 | Ibrahim Danlami | Kenya |
27 | Ibrahim Adeola Mopelola | Cotonou, Benin |
28 | Ayeni Adebayo Emmanuel | Brussels, Belgium |
29 | Akande Eahab Adekola | Berne, Switzerland |
30 | Arewa Esther | Windhoek, Namibia |
31 | Gergadi Joseph John | Libreville, Gabon |
32 | Luther Ogbomode Ayo-Kalata | Sierra-Leone |
33 | Danladi Yakubu Nyaku | Khartoum, Sudan |
34 | Bello Dogon-Daji Haliru | Bangkok, Thailand |
Shugaba Tinubu ya ba ma'aikatar harkokin waje umarnin fara gudanar da taron bita ga sababbin jakadun cikin gaggawa.
Wannan naɗi ya zo ne bayan da masu sukar gwamnati suka koka kan cewa rashin jakadu na haifar da giɓi a wakilcin Najeriya a idon duniya.
Karanta sanarwar a nan kasa:
Jakadu da Tinubu ya naɗa sun shiga matsala
A wani rahoto, mun ruwaito cewa, wasu ƙasashe na iya ƙin karɓar jakadun shugaban Najeriya, Bola Tinubu saboda ƙarancin lokacin wa’adin mulkinsa.
A halin yanzu, ma’aikatar harkokin waje na fama da samun yarjejeniyar karbar jakadun yayin da zaɓen 2027 ke gabatowa, abin da ke sa ƙasashen waje nuna jinkiri.
Tun da ma can, masana diflomasiyya sun ce jinkirin nadin jakadu kuskure ne, kuma hakan na iya rage tasirin Najeriya a hulɗar ƙasa da ƙasa.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


