Majalisar Dokoki Ta Fara Shirin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano, Aminu Gwarzo
Kano, Nigeria - Majalisar dokokin jihar Kano ta fara shirin tsige mataimakin gwamna, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo a zamanta na yau Alhamis, 5 ga Maris, 2026.
Majalisar dokokin ta fara wannan yunkuri ne bisa zargin Aminu Gwarzo da hannu a badakalar kudin al'umma lokacin da yake rike da kwamishinan kananan hukumomi a jihar Kano.

Source: Twitter
Majalisa ta fara shirin tsige Aminu Gwarzo
Jaridar Aminiya ta tattaro cewa ‘yan majalisar sun ce zarge-zargen na da nasaba da yadda aka gudanar da wasu harkokin kudi, wanda suke ganin ya saba wa ka’idojin shugabanci nagari.
Shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin Kano, Hon. Lawan Hussaini Dala, ne ya gabatar da takardar kudirin tsige mataimakin gwamnan a zaman yau Alhamis.
Ya bayyana cewa matakin ya samo asali ne daga tanadin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, musamman sashe na 188 da ya tanadi yadda ake tsige manyan jami’an gwamnati.
Zarge-zargen da ake wa mataimakin Abba

Kara karanta wannan
Khamenei: An ɗage taron jana'izar jagoran addini a Iran yayin da ake harin magajinsa
A cewarsa, zarge-zargen sun shafi lokacin da Aminu Gwarzo ya rike mukamin Kwamishinan Kananan Hukumomi na Kano tsakanin 2023 zuwa 2024, da harkokin ofishinsa na mataimakin gwamna.
Hon. Lawan Dala ya bayyana cewa a lokacin da yake jagorantar ma’aikatar kananan hukumomi 44 na Kano, an zarge shi da karbar Naira miliyan 1.5 duk wata daga kowace karamar hukuma tsakanin watan Yunin 2023 zuwa Janairun 2024.
Wannan, a cewarsa, ya kai kimanin Naira miliyan 66 a kowane wata, wanda jimillarsa gaba daya ta kai kusan Naira miliyan 462.
Bayan wannan kuma, shugaban masu rinjaye ya ce daga watan Fabrairu zuwa Yulin 2024, ana zargin kowace karamar hukuma ta sake ware wa Aminu Gwarzo Naira miliyan 3.255 a wata da sunan gudanar da wasu ayyuka na musamman.
A cewarsa, kudin da aka tarawa mataimakin gwamnan a cikin watanni shida sun kai kusan Naira miliyan 726.
Majalisa ta fara cika sharuddan tsigewa
Ya ce irin wadannan mu’amaloli sun saba wa dokokin gudanar da kudaden gwamnati, kuma suna daga cikin manyan laifuffuka a karkashin kundin tsarin mulki, domin sun karya amana da ka’idojin da ake bukata daga jami’in gwamnati.
Lawan Dala ya kuma bayyana cewa ‘yan majalisa 38 ne suka sanya hannu kan kudirin tsige mataimakin gwamnan, abin da ya cika sharadin da doka ta tanada domin fara wannan tsari.
Shugaban majalisar, Rt. Hon Isma'ila Falgore ya amshi takardar kudirin, kuma ana sa ran za a mika ta ga mataimakin gwamnan domin ya kare kansa bisa tsarin da doka ta gindaya.

Source: Facebook
Legit Hausa ta tuntubi mai magana da yawun Majalisar dokokin Kano, Kamaludden Sani Shawai, wanda ya tabbatar mana da cewa an gabatar da tuhume-tuhumen da ake wa Aminu Gwarzo.
Shawai ya shaidawa wakilinmu ta wayar tarho cewa labarin da wasu jaridu ke yadawa cewa an tsige mataimakin gwamnan ba gaskiya ba ne, domin dole sai an bi matakai.
"Abin da ya faru shi ne gabatar da takarda ta tuhume-tuhume, wadanda ake wa mataimakin gwamnan Kano, amma ba wai an tsige shi ba, akwai matakai da za a bi bisa kundin tsarin mulki," in ji shi.
Kwamishina ya yi murabus a Kano
A wani rahoton, kun ji cewa Hon. Umar Haruna Doguwa ya yi murabus daga kujerar kwamishinan Albarkatun Ruwa na jihar Kano.

Kara karanta wannan
Yadda kisan Khamenei zai shafi 'yan Shi'a a Najeriya, rashinsa ya 'hada' kan Musulmi
Gwamna Abba ya amince da murabus din kwamishinan, tare da yaba masa bisa gudummuwar da ya ba gwamnatinsa da al'ummar Kano.
Abba ya masa fatan alheri a ayyukansa na gaba, sannan ya tabbatar da cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da dora wa kan nasarorin da aka samu a bangaren albarkatun ruwa.
Asali: Legit.ng
