Ramadan: Lakurawa Sun Bude Wuta a Masallaci, Sun Kashe Mutane ana Sallar Tarawihi
- Yan ta'addan Lakurawa sun kai farmaki wani masallaci yayin da mutane ke tsakiyar gudanar da sallar tarawihi a jihar Kebbi
- Rahotanni sun nuna cewa lamarin, wanda ya faru a garin Dadin Kowa da ke karamar hukumar Maiyawa, ya yi ajalin mutane da dama a daren jiya Laraba
- Babu wata sanarwa a hukumance, amma mazauna garin sun tabbatar wa Legit Hausa faruwar lamarin a watan azumin Ramadan
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Kebbi, Nigeria - Rahotanni sun nuna cewa 'yan ta'addan kungiyar Lakurawa sun kai mummunan hari kan mutane suna tsakiyar sallar tarawihi a jihar Kebbi.
Bayanai sun nuna cewa 'yan ta'addan sun bude wa masallata wuta suna cikin sallah a daren jiya Laraba a garin Dadin Kowa da ke yankin karamar hukumar Maiyama ta jihar Kebbi.

Source: Original
Wani mai amfani da kafar sada zumunta ta X, Bakatsine, wanda ya saba kawo labaran matsalar tsaro, ya tabbatar da faruwar lamarin a shafinsa da safiyar yau Alhamis.
Lakurawa sun kashe mutane a masallaci
Ya ce maharan sun far wa mutanen suna tsaka da sallar tarawihi, ibadar da musulmi ke yi a watan azumin Ramadan domin neman yardar Allah SWT.
Rahoto ya nuna cewa an kashe mutane da dama, wasu da yawa kuma sun jikkata, sannan an keta alfarmar masallaci wanda yake matsayin wuri mai tsarki ga musulmi.
"A daren jiya, wasu mayakan Lakurawa sun far wa al’ummar garin Dadin-Kowa da ke karamar hukumar Maiyama a Jihar Kebbi, inda suka kai hari kan mazauna garin yayin da suke gudanar da sallar Tarawihi.
"A harin, an kashe mutane da dama, wasu da yawa kuma sun jikkata, sannan an keta alfarmar masallaci wanda yake matsayin wuri mai tsarki."
An tabbatar da mutuwar mutum 4
Masani kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a Najeriya, Zagazola Makama ya tabbatar da faruwar lamarin a shafinsa na X.
Ya ce mutane hudu ne suka rasa rayukansu a harin, wanda ake zargin mayakan Lakurawa sun kaddamar domin daukar fansar abin da sojoji suka masu.
"Majiyoyi sun ce maharan sun kutsa garin, suka bude wuta kan masallata, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane hudu, yayin da wasu biyar suka samu raunuka daban-daban.
"An garzaya da wadanda suka jikkata zuwa wani asibiti domin neman magani," in ji Zagazola Makama.
An kashe 'dan agajin Izala a harin
Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da aukuwar lamarin ga wakilin Legit Hausa, ya ce ba a kammala tantance yawan wadanda suka mutu ba.
Matashin ya tabbatar da cewa abokinsa, 'dan agajin JIBWIS na cikin wadanda aka kashe a harin, inda ya yi addu'ar Allah Ya karbi shahadarsa.

Source: Facebook
"A daren jiya ne Lakurawa suka kashe abokina a masallaci, na samu labarin 'yan uwa da dama sun rasa rayukansu, muna rokon addu'o'in ku, Allah Ya jikanshi Ya gafarta mashi da dukkan musulmi," in ji shi.
Sojoji sun dakile harin mayakan Lakurawa
A wani rahoton, kun ji cewa an gwabza fada tsakanin dakarun sojojin Najeriya da 'yan ta'addan kungiyar Lakurawa a jihar Kebbi da ke yankin Arewa maso Yamma.
Rahotanni sun nuna cewa an yi wannan artabu ne lokacin mayakan Lakurawa suka farmaki tawagar kwamandan rundunar Operation Fansan Yamma, Manjo Janar Bemgha Koughna.
Dakarun sojojin sun yi musayar wuta da 'yan ta'addan inda suka hallaka da dama daga cikinsu tare da kwato makamai da dama daga hannunsu.
Asali: Legit.ng


