El Rufai Ya Sake Kinkimo Rigima a cikin Watan Azumi, Ya Maka ICPC a gaban Kotu
- Malam Nasir El-Rufai ya shigar kara gaban kotu kan samamen da hukumar ICPC ta kai gidansa na Abuja a ranar 4 ga watan Fabrairu, 2026
- Tsohon gwamnan ya bukaci kotun ta ba da umarnin a biya shi diyyar Naira biliyan daya saboda bata masa suna da shiga gidansa ba bisa ka'ida ba
- El-Rufai ya gabatar da hujjojinsa a gaban kotu a kokarin tabbatar da cewa samamen da aka kai gidansa ya sabawa kundin tsarin mulki
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma daya daga cikin jagororin jam'iyyar hadaka, ADC, Malam Nasir El-Rufai ya tattago rigimar shari'a da hukumar yaki da rashawa ta ICPC.
El-Rufai ya maka hukumar ICPC a gaban kotu kan samamen da ta kai gidansa da ke babban birnin tarayya Abuja, wanda ya bayyana a matsayin karya doka.

Source: Facebook
El-Rufai ya nemi diyyar N1bn daga ICPC
Jaridar Vanguard ta ce El-Rufai, ya shigar da ƙarar hukumar ICPC tare da neman ta biya shi diyya ta Naira biliyan ɗaya bisa zargin mamaye gidansa da ta yi ba bisa ka’ida ba.
El-Rufai ya shigar da wannan kara a gaban babbar kotun tarayya ta Abuja ta hannun lauyoyinsa ƙarƙashin jagorancin Oluwole Iyamu, SAN.
Ya roƙi kotu ta ayyana sammacin bincike da Kotun Majistare ta bayar ranar 4 ga Fabrairu, 2026 wanda ya ba da izinin bincike da kwace kayayyaki a gidansa, a matsayin wanda ya saba doka.
Abubuwan da El-Rufai ya nema a kotu
Ya buƙaci kotu ta ayyana cewa sammacin binciken “ba shi da inganci saboda rashin fayyace bayanai, kurakuran rubutu, rashin bayyana yadda za a aiwatar da shi, wuce gona da iri, da kuma rashin dalili mai gamsarwa.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa tsohon gwamnan ya shigar da ƙarar ta hanyar takardar ƙorafi mai lamba FHC/ABJ/CS/345/2026, inda ya sanya ICPC a matsayin wanda ake ƙara na farko.
El-Rufai ya kuma sanya Alkalin Kotun Majistare ta Abuja; Sufeto Janar na ’Yan Sanda (I-G); da Antoni Janar (AGF) a matsayin waɗanda ake ƙara na biyu zuwa na huɗu.
A cikin ƙarar da aka shigar ranar 20 ga Fabrairu, tsohon gwamnan, wanda ake tsare da shi, ya nemi abubuwa bakwai daga kotu, kamar yadda Daily Post ta kawo.

Source: Twitter
El-Rufai ya nemi a dawo da kayan gidansa
Ya roƙi kotu ta ayyana cewa samame tare binciken gidansa da ke House 12, Mambilla Street, Aso Drive, Abuja, ranar 19 ga Fabrairu da misalin ƙarfe 2:00 na rana, ya saba wa kundin tsarin mulki.
Haka kuma El-Rufai'i ya nemi kotu ta yi umarnin da zai tilasta wa ICPC da Sufetan Yan Sanda mayar masa da duk kayayyakin da aka kwace daga gidansa.
Bugu da ƙari, tsohon gwamnan ya nemi kotu ta umarci a biya shi Naira biliyan ɗaya a matsayin diyyar shiga gidansa ba bisa ka'ida ba, kwashe masa kaya, ɓacin rai, tozarci, damuwa, take sirri da ɓata masa suna.
Yadda ICPC ta kai samame gidan El-Rufai
A bayan, kun ji cewa jami'an hukumar ICPC sun kai samame gidan tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai da ke Abuja domin gudanar da bincike.
Mai magana da yawun El-Rufai, Muyiwa Adekeye, ya bayyana cewa jami'an ICPC sun kai samame tare da gudanar da bincike a gidan tsohon gwamnan.
Lauyan Nasir El-Rufai ya bayyana cewa binciken da aka yi a gidan tsohon gwamnan ya saba wa doka da take hakkin dan adam.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


