Kai Ruwa Rana da Ake Yi Tsakanin El-Rufai da Gwamnatin APC, abin da Muka Sani

Kai Ruwa Rana da Ake Yi Tsakanin El-Rufai da Gwamnatin APC, abin da Muka Sani

Abuja - Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, Malam Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna (2015-2023) yana tsare a hannun hukumar yaki da rashawa ta ICPC.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

A cikin wata sanarwa da ICPC ta fitar a ranar 19 ga Fabrairu, 2026, hukumar ta ce El-Rufai na tsare a hannunta ne daga ranar 18 ga Fabrairu, 2026.

Takun sakar da ake yi tsakanin El-Rufai da gwamnatin APC
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai a dakin karatu. Hoto: @MuyiwaAdekeye
Source: Twitter

Takun sakar El-Rufai da gwamnatin APC

A sanarwar da ICPC ta wallafa a shafinta na X, dauke da sa hannun shugaban sashen hulda da jama'a da watsa labarai, John Okor, Odey, hukumar ta ce:

"Malam Nasiru El-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna yana tsare a hannunmu ya zuwa lokacin tashi aiki a yau, Laraba 18 ga Fabrairu, 2026... bisa wani bincike da ake yi."

A cikin wannan rahoto, Legit Hausa ta yi nazari kan kai ruwa rana da ake yi tsakanin El-Rufai da gwamnatin APC, karkashin Shugaba Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Jami'an ICPC sun kai samame gidan El Rufai, sun je neman wani abu

1. Alakar El-Rufai da APC da zaben 2023

Alakar El-Rufai da gwamnatin APC ta lalacewa bayan tsohon gwamna ya gaza samun mukamin minista.
Shugaba Bola Tinubu (hagu) da Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna (dama). Hoto: @officialABAT, @elrufai
Source: Facebook

Malam Nasir El-Rufai ya kasance daya daga cikin mambobin da suka kafa jam’iyyar APC kuma babban jigo ne a cikinta.

Lokacin yakin neman zaben shugaban kasa na 2023, ya taka rawar gani sosai wajen tattara goyon baya ga dan takarar lokacin, Bola Tinubu, musamman a yankin Arewa.

A wata hira da BBC Hausa ta wallafa a shafinta na intanet a ranar 13 ga watan Fabrairu, 2026, El-Rufai ya fito fili ya bayyana cewa ba shi da wata alaka ta kashin kansa da Shugaba Tinubu.

Kuma ya ce ya goyi bayan takarar Tinubu ne kawai saboda haduwarsu karkashin jam’iyyar APC, inda ya bambanta hakan da kusancin da ke tsakaninsa da tsohon Shugaba Muhammadu Buhari.

Ya bayyana cewa:

“Ni Tinubu ba mu taba wani sha'ani da shi ba, ni Tinubu ba mutumina ba ne, ba abokina ba ne, ba mu yi siyasa tare ba, a APC muka hadu."

Kara karanta wannan

"Babu ruwan DSS," An ji wadanda suka cafke El Rufai bayan Ya bar hannun EFCC

'Yar alakar da ke tsakaninsu ta fara tabarbarewa ne bayan zaben 2023. Shugaba Tinubu ya nada El-Rufai a matsayin minista, sai dai majalisar dattawa ta ki tabbatar da shi a watan Oktoban 2023.

Daga nan ne El-Rufai ya rikide zuwa mai sukar manufofin gwamnatin Tinubu, inda ya fara sauya sheka zuwa jam’iyyar SDP kafin ya koma jam’iyyar ADC ta hadakar 'yan adawa.

Wannan sauyin sheka ya sanya shi a sahun gaba wajen adawa, wanda hakan ya kara fadada barakar siyasa dake tsakaninsa da jam’iyyar APC mai mulki.

2. Yunkurin kama El-Rufai a filin jirgi

Jami'an tsaro sun yi yunkurin kama El-Rufai a filin jirgin sama na Abuja.
Malam Nasir El-Rufau yana magana da jami'an tsaron da suka yi yunkurin kama shi a filin jirgi. Hoto: @MuyiwaAdekeye
Source: Facebook

Takun saka ya fara karfi ne a ranar 12 ga watan Fabrairu, 2026, inda jami’an tsaro sun yi yunkurin cafke El-Rufai bayan saukarsa a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja, daga birnin Cairo.

Kamar yadda hadimin sa kan yada labarai, Muyiwa Adekeye, da lauyansa, Ubong Akpan suka bayyana, jami’an sun tunkari tsohon gwamnan ne ba tare da nuna masa takardar sammaci ko gayyata ta hukuma ba.

El-Rufai ya ki amincewa da bukatar jami’an, lamarin da ya janyo hatsaniya, inda Legit Hausa ta rahoto cewa fasinjoji da sauran jama’ar da ke kusa suka taru suka hana a tafi da shi.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: Jami'an DSS sun cafke El Rufai a harabar ofishin EFCC

A yayin wannan dambarwar, jami’an sun kwace fasfo din tsohon gwamnan na fita kasashen waje daga hannun daya daga cikin hadimansa.

3. Batun nadar kiran wayar Ribadu

A hira da Arise News, El-Rufai ya yi zarge-zarge game da Nuhu Ribadu
Malam Nuhu Ribadu a dakin watsa shirye-shirye na Arise News a Abuja. Hoto: @elrufai
Source: Twitter

Bayan abin da ya faru a filin jirgin sama, El-Rufai ya bayyana a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV a ranar 13 ga watan Fabrairu, 2026.

A cikin wannan hira da aka yi kai-tsaye, ya sanar da aniyarsa ta mika kansa ga EFCC da kansa a ranar Litinin, 16 ga watan Fabrairu, domin amsa tuhume-tuhumen da ake masa na cin hanci da rashawa.

Haka kuma, ya fadi wasu zarge-zarge masu tada hankali game da Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA), Nuhu Ribadu.

Malam Nasir El-Rufai ya bayyana cewa ya samu damar sauraron (ko kuma an sanar da shi) wata tattaunawar waya da aka nada, inda aka ji Ribadu yana bai wa jami'an tsaro umarnin su kama shi.

Ya danganta wannan umarni kai-tsaye da yunkurin da aka yi na kama shi a filin jirgin sama ranar 12 ga watan Fabrairu, inda ya ce:

Kara karanta wannan

Manyan jam'iyyar APC da aka gani wajen tarbar gwamna Abba daga NNPP a Kano

"Nuhu Ribadu ne ya yi kiran sannan ya ba da umarnin lallai sai an tsare ni... Wani ne ya nada muryarsa a waya sannan ya gaya mini."

Ya bayyana cewa gwamnati na tunanin ita kadai ce ke da ikon saurare ko nada kiran waya, amma ya jaddada cewa su ma 'yan adawa suna da irin wannan fasahar.

4. Zargin shigo da Thallium da martanin Ribadu

A ranar 30 ga Fabrairu, 2026, Malam Nasir El-Rufai ya aika wa Nuhu Ribadu wasikar neman bahasi a hukumance game da rahoton cewa ofishinsa ya sayo kimanin kilogiram 10 na sinadarin thallium sulphate.

El-Rufai ya wallafa wasikar a shafinsa na X, inda ya bayyana binciken nasa a matsayin wani abu da ya shafi "tsaron jama’a, bin ka’idojin dimokuradiyya... da kuma tabbatar da amana."

A wasikar, ya yi tambaya game da manufar sayo sinadarin, inda za a adana shi, da kuma ko an sanar da hukumomi irin su NAFDAC da NCDC.

Ofishin Ribadu ya mayar da martani ta wata wasika mai kwanan wata 13 ga watan Fabrairu, 2026 wadda Birgediya Janar O.M. Adesuyi ya sanya wa hannu, in ji rahoton Premium Times.

Kara karanta wannan

Yadda jama'a suka fito zanga zanga da El Rufa'i ya ziyarci EFCC

NSA ya ya musanta sayo ko shigo da wannan sinadari yayin da ya mika maganar ga hukumar DSS domin ci gaba da bincike, tare da fadawa El-Rufai ya shirya gabatar da hujjojinsa ga hukumar.

5. El-Rufai ya kai kansa EFCC

Malam Nasir El-Rufai ya mika kansa ga hukumar EFCC
Malam Nasir El-Rufai a cikin mota jim kadan bayan ya isa ofishin EFCC a Abuja. Hoto: @MuyiwaAdekeye
Source: Twitter

A ranar 16 ga watan Fabrairu, 2026, wadda ta yi daidai da ranar cikarsa shekaru 66 da haihuwa, Malam Nasir El-Rufai ya mika kansa ga hukumar EFCC a hedikwatarta dake Abuja.

An tsare shi tare da yi masa tambayoyi kan zargin bacewar kimanin N423bn na jihar Kaduna a lokacin da yake gwamna, kamar yadda yake kunshe cikin rahoton kwamitin bincike na musamman na majalisar dokokin jihar Kaduna na shekarar 2024.

Jaridar Guardian, ta rahoto cewa tsohon gwamnan na Kaduna ya shafe kwanaki a tsare a hannun EFCC (daga Litinin zuwa yammacin Laraba).

6. DSS ta yi karar El-Rufai

Ana cikin hakan, sai hukumar DSS ta shigar da kara kan tuhume tuhume uku a kan El-Rufai a gaban Babbar Kotun Tarayya dake Abuja, bisa zargin tafka laifukan yanar gizo da kuma barazana ga tsaron kasa.

Kara karanta wannan

El Rufa'i ya amsa gayyata, zai kai kansa ofishin EFCC a yau

Tuhume tuhumen, karkashin lambar shigar da kara ta FHC/ABJ/CR/99/2026, sun zargi El-Rufai da yin kutse ta haramtacciyar hanya a tattaunawar wayar Ribadu, da kuma sanin mutumin da ya yi wannan kutse tare da yin harka da shi ba tare da ya kai rahoto ga hukumomi ba.

Wadannan laifuka sun saba wa dokar hana aikata laifuka ta yanar gizo, 2024, da kuma dokar sadarwa ta Najeriya, 2003.

An tsara cewa za a gurfanar da shi a gaban kotun ranar 25 ga watan Fabrairu, 2026, kamar yadda jaridar The Cable ta rahoto.

7. Belin EFCC da shiga hannun ICPC

A ranar Laraba, 18 ga watan Fabrairu, 2026, da misalin karfe 8 na dare, hukumar EFCC ta amince ta ba Malam Nasir El-Rufai beli bayan kwanaki uku ana yi masa tambayoyi.

Sai dai, yayin da yake shirin barin harabar ofishin EFCC, wasu dakaru dauke da makamai suka sake cafke shi nan take, in ji rahoton Legit Hausa.

Rahotannin farko da shaidun gani da ido sun yi nuni da cewa jami'an DSS ne suka kama shi, amma daga baya hukumar ICPC ta bayyana cewa jami’anta ne suka kama shi.

8. Tsare shi da samamen gidansa na Abuja

Kara karanta wannan

Shigo da guba: DSS za ta titsiye El Rufa'i kan zargin da ya yi wa Ribadu

ICPC ta kai samame gidan El-Rufai.
Malam Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna wanda ke tsare a hannun hukumar ICPC. Hoto: @elrufai, @icpcnigeria
Source: Twitter

Hukumar ICPC ta tabbatar da cewa El-Rufai yana hannunsu a ranar 19 ga watan Fabrairu, inda ta bayyana cewa zai ci gaba da zama a can domin "bincike dake gudana" dangane da lokacin mulkinsa na gwamna.

Kwanaki biyu da suka gabata ne Legit Hausa ta rahoto cewa, jami’an hukumar ta ICPC sun kai samame gidan El-Rufai dake unguwar Aso Drive a Abuja.

Hadiminsa kan yada labarai, Muyiwa Adekeye, ne ya sanar da gudanar da binciken a shafinsa na X, inda ya tabbatar da cewa jami’an sun kai samame don nema wasu abubuwa a gidan.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa an kai samamen ne a daidai lokacin da El-Rufai yake riga yana tsare a hannun hukumar ta ICPC.

9. Martanin lauyoyin El-Rufai

Babban lauyan El-Rufai, Ubong Akpan, ya yi Allah-wadai da samamen da ICPC ta kai gidansa, inda ya bayyana shi a matsayin "haramtaccen mataki kuma take dokokin shari'a da hakkokin bil'adama."

Kara karanta wannan

Babbar magana: Ganduje ya yi magana kan batan Dadiyata, ya maida martani ga El Rufai

Shi da tawagar sa ta lauyoyi sun lashi takobin kalubalantar tsare shi da kuma binciken da aka yi ta hanyar amfani da hanyoyin da suka dace a kotu.

Jaridar Vanguard ta nakalto kalaman Akpan, inda ya bayyana cewa tawagar lauyoyin tana kokarin shigar da bukatar neman beli da kuma karar neman kariya ga hakkokin dan adam.

Jiga-jigan jam’iyyar ADC sun goyi bayan kiran da ake yi na cewa lallai a gurfanar da El-Rufai a gaban kotu ko kuma a sake shi nan take, inda suka bayyana jerin kame-kamen da ake yi masa a matsayin "farautar siyasa."

10. Abubuwan da ka iya faruwa nan gaba

A mako mai zuwa, hukumar DSS za ta gurfanar da Malam Nasir El-Rufai, kan tuhume-tuhumen laifukan yanar gizo.

Sannan, a makonni masu zuwa, hukumomin EFCC da ICPC na iya gurfanar da tsohon gwamnan bayan kammala bincike kan kudaden jihar Kaduna.

Ya zuwa yau 22 ga watan Fabrairu, 2026, El-Rufai yana ci gaba da zama a hannun hukumar ICPC ba tare da tabbas kan ranar da za a sake shi ba.

Jigon ADC ya kausasa harshe kan El-Rufai

Kara karanta wannan

El Rufai zai tsaya takarar shugaban Najeriya a 2027? Tsohon gwamna ya bada amsa

A wani labari, mun ruwaito cewa, jigo a jam’iyyar ADC, Usman Austin, ya mika bukatarsa ga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC kan Nasir El-Rufai.

Usman Austin ya bukaci ICPC da ta gaggauta gurfanar da tsohon gwamnan na Kaduna, a gaban kotu ko kuma ta sake shi ya kama hanyar gaban shi.

Ya jaddada cewa idan har akwai zarge-zarge a kan El-Rufai, to kamata ya yi a kai su gaban kotu, yana mai nuna mahimmancin bin tabbatattun matakai na shari’a.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com