Ta Faru Ta Kare: Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu kan Sabuwar Dokar Zabe
Abuja - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu kan kudurin dokar zaɓe ta shekarar 2026 (wacce aka sabunta daga dokar ta 2022) domin ta zama doka a hukumance.
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Wannan mataki ya biyo bayan amincewa da kudirin dokar da Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta yi a ranar Talata, bayan kwashe watanni ana tattaunawa da muhawara a kai.
Ana kallon sabuwar dokar, wacce ta soke dokar zaɓe ta shekarar 2022, a matsayin wani yunƙuri na ƙara gyara tsarin zaɓen ƙasar gabanin babban zaɓen 2027 mai zuwa, in ji rahoton Channels TV.
Akwai ƙarin bayani nan gaba...
Asali: Legit.ng