Magudi: Limamin Coci Ya Fadi Amfanin Yin Zabe Ana Azumi a Watan Ramadan

Magudi: Limamin Coci Ya Fadi Amfanin Yin Zabe Ana Azumi a Watan Ramadan

  • Wani malamin addini, Sam Olu-Alo, ya goyi bayan jadawalin zaɓen 2027, yana mai fadan fa'idar yin zaben a watan azumi
  • Malamin ya ce gudanar da zaɓe a lokacin azumin Musulmi zai ƙara tsoron Allah da gaskiya ga masu zaɓe da ’yan siyasa
  • Ya roƙi ’yan Najeriya su guji nuna wariyar addini, su mai da hankali kan zaman lafiya da haɗin kai yayin zaɓukan 2027

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Wani malamin addini a Najeriya, Fasto Sam Olu Alo, ya yi magana bayan Musulmi na neman sauya ranar zabe saboda Ramadan.

Fasto Alo ya nuna goyon bayansa ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) kan ranar da ta sanya domin gudanar da babban zaɓen shekarar 2027.

Fasto ya goyi bayan yin zabe a Ramadan
Shugaban hukumar INEC, Joash Amupitan. Hoto: INEC Nigeria.
Source: Facebook

Malamin ya bayyana cewa gudanar da zaɓe a lokacin azumin Musulmi zai kasance alheri ga ƙasa baki ɗaya, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Jerin sharudda 15 da Sarkin Musulmi ya gindaya wa malaman da za su yi tafsiri a Ramadan

Ya jaddada cewa irin wannan lokaci mai tsarki zai taimaka wajen rage magudin zaɓe tare da ƙarfafa gaskiya a tsakanin masu kaɗa ƙuri’a da ’yan siyasa.

Ranar da hukumar zabe ta sanya

Legit Hausa ta ruwaito cewa INEC ta sanar da cewa za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa, ’yan Majalisar Tarayya a ranar 20 ga Fabrairu, 2027, yayin da na gwamnoni da ’yan Majalisun Jihohi za su gudana a ranar 6 ga Maris, 2027.

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ne ya bayyana jadawalin zaɓen a wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja.

Fasto ya fadi amfanin yin zabe a Ramadan
Fasto Sam Olu-Alo da Shugaban INEC, Joash Amupitan. Hoto: Prophet Sam Olu Alo, INEC Nigeria.
Source: Facebook

Fasto ya soki masu korafi kan ranar zabe

Bayan kammala azumi da addu’o’in kwanaki 41 na cocinsa, Olu Alo ya yi watsi da korafe-korafen da wasu ke yi kan gudanar da zaɓe a lokacin azumi.

Ya ce:

“A lokacin azumi muna ƙarfafa gaskiya, kuma hakan ba zai ba mu damar murɗe abubuwa ba. Ina ganin ya dace a gudanar da zaɓe a lokacin azumi domin hakan zai taimaka mana mu zaɓi shugabanninmu cikin addu’a.”

Ya ƙara da cewa bai kamata a tada jijiyoyin wuya ba kan ranar da aka sanya domin babban zaɓen ba, yana mai cewa an taɓa gudanar da zaɓe a lokacin azumin Kiristoci ba tare da wata hayaniya ba.

Kara karanta wannan

Gwamnan APC da ake fatan ya zama shugaban majalisar dattawa bayan 2027

A cewarsa, bai kamata a ɗaga murya ba idan jadawalin ya faɗa a lokacin azumin Musulmi, domin hakan ma zai taimaka wajen gudanar da zaɓe cikin tsoron Allah da gaskiya, ba tare da nuna wariyar addini ba, cewar The Guardian.

Yadda INEC ta sauya ranar zabe saboda Kiristoci

Mun ba lu labarin cewa an tuna yadda hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC ta sauya lokacin zabe bayan Kiristoci sun yi korafi.

A shekarar 2003, INEC ta sauya ranar zaben gwamna da majalisar jiha bayan korafin Fastoci na Katolika kan karo da bikin Easter.

Kungiyar CBCN ta ce sanya zabe a ranar Asabar Mai Tsarki ya nuna rashin la’akari da mabiya Kirista masu bin addinin da ibada sau da kafa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.