Gwamnatin Tinubu Ta Tallafawa 'Yan Kasuwar da Suka Yi Asara a Gobarar Kano
- Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya je jihar Kano domin jajantawa 'yan kasuwar da gobara ta jawo musu asara
- Kashim Shettima ya sanar da cewa gobarar wadda ta lakume shaguna masu dumbin yawa babbar masifa ce da ta shafi kasa baki daya
- Hakazalika, mataimakin shugaban kasar ya sanar da tallafin da gwamnatin tarayya ta ba 'yan kasuwar da mummunar gobarar ta ritsa da su
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Kano - Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ta ba da tallafi ga 'yan kasuwar da gobara ta ritsa da su a Kano.
Gwamnatin tarayya ta sanar da ba da tallafin Naira biliyan 5 ga mutanen da gobarar da ta tashi kwanan nan a Kasuwar Singer da ke Kano ta shafa.

Source: Facebook
Jaridar Daily Trust ta ce mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ne ya bayyana wannan tallafin a ranar Litinin, 16 ga watan Fabrairun 2026.
Kashim Shettima ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar jajantawa da ya kai kasuwar, inda aka yi asarar kayayyaki da dukiyoyi na biliyoyin Naira sakamakon gobarar.
Gobara ta yi barna a Kano
Gobarar wadda ta fara ranar Asabar, ta ci gaba da ci har zuwa ranar Lahadi, inda ta kone shaguna da rumfuna sama da 1,000 a ɗaya daga cikin manyan wuraren kasuwancin Nijeriya.
Hukumar kashe gobara ta ce har yanzu tana gudanar da bincike domin gano sanadin gobarar da kuma girman asarar da ƴan kasuwar suka yi.
Shettima ya jajanta kan gobarar Singer
Mataimakin shugaban kasar wanda ya siffanta lamarin a matsayin babbar masifa, ya ce rashi ne ba ga Jihar Kano kaɗai ba, har ma ga daukacin Najeriya, jaridar Daily Post ta kawo labarin.
Ya yi wa waɗanda abin ya shafa addu’a tare da roƙon Allah da ya kiyaye aukuwar irin wannan masifa a nan gaba.
A yayin ziyarar, mataimakin shugaban ƙasar ya samu rakiyar gwamnonin jihohin Jigawa, Kebbi, da Imo.

Source: Facebook
Za a yi adalci wajen rabon tallafin
Shugaban kungiyar ƴan kasuwar Singer, Junaid Zakari, ya jinjina wa gwamnatin Tltarayya kan abin da ya kira tallafi mai kyan gaske wanda ya zo a kan gaba.
Ya tabbatar da cewa za a yi amfani da kuɗaɗen cikin adalci domin tallafa wa ƴan kasuwar da abin ya shafa da kuma farfaɗo da harkokin kasuwanci a kasuwar.
Bayan ziyarar kasuwar, Mataimakin Shugaban Ƙasar ya wuce zuwa filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata, Kano, domin taron karɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf, a hukumance zuwa jam’iyyar APC.
Shugaba Tinubu ya tafi jihar Adamawa
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tafi wata ziyarar aiki zuwa jihar Adamawa da ke yankin Arewa maso Gabas na Najeriya.
Shugaba Tinubu zai ƙaddamar da ayyuka da dama a Adamawa ƙasa da sa'o'i 48 bayan ya kai irin wannan ziyarar zuwa jihar Kebbi.
Yayin ziyarar ta yini ɗaya, shugaban zai buɗe manyan ayyuka, ya haɗu da manyan jami'an gwamnati, sannan ya gana da sarakunan gargajiya na jihar.
Asali: Legit.ng

