An Zo wajen: Gwamnatin Abba Ta Yi Magana kan Batun Hana Kwankwaso zuwa Kano

An Zo wajen: Gwamnatin Abba Ta Yi Magana kan Batun Hana Kwankwaso zuwa Kano

Jihar Kano - Gwamnatin jihar Kano ta yi martani kan zargin da ke cewa tana shirin hana Rabiu Musa Kwankwaso cikinta.

Gwamnatin ta musanta ikirarin da ake yi na cewa tana Kwankwaso, shiga jihar, inda ta siffanta zargin a matsayin ƙarya kuma kokari ne na yaudarar jama’a da gangan.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Waiya, ya fitar a ranar Alhamis, 12 ga watan Fabrairun 2026.

Wannan musantawar ta biyo bayan wasu kalamam da aka ce sun fito ne daga bakin makusancin Kwankwaso, Buba Galadima.

Buba Galadima dai ya bayyana cewa gwamnatin Gwamna Abba Yusuf ta rubuta wa gwamnatin tarayya takarda domin ta dakatar da Kwankwaso daga ziyartar Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng