An Zo wajen: Gwamnatin Abba Ta Yi Magana kan Batun Hana Kwankwaso zuwa Kano
Jihar Kano - Gwamnatin jihar Kano ta yi martani kan zargin da ke cewa tana shirin hana Rabiu Musa Kwankwaso cikinta.
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Gwamnatin ta musanta ikirarin da ake yi na cewa tana Kwankwaso, shiga jihar, inda ta siffanta zargin a matsayin ƙarya kuma kokari ne na yaudarar jama’a da gangan.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Waiya, ya fitar a ranar Alhamis, 12 ga watan Fabrairun 2026.
Wannan musantawar ta biyo bayan wasu kalamam da aka ce sun fito ne daga bakin makusancin Kwankwaso, Buba Galadima.
Buba Galadima dai ya bayyana cewa gwamnatin Gwamna Abba Yusuf ta rubuta wa gwamnatin tarayya takarda domin ta dakatar da Kwankwaso daga ziyartar Kano.
Asali: Legit.ng