Bayan Abin da Ya Faru a Filin Jirgi, El Rufai Zai Gurfana a Gaban Hukumar EFCC
- Lauyan Malam Nasiru El-Rufai ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan zai amsa gayyatar EFCC a ranar Litinin, 18 ga watan Fabrairu, 2026
- Barista Ubong Esop Akpan ya bayyana hakan ne jim kadan bayan yunkurin da jami'an tsaro suka yi na kama El-Rufai a filin jirgin sama a Abuja
- Ya ce abin da jami'an tsaron suka yi ya saba wa tanadin kundin tsarin mulki, yana mai cewa sun sanar da EFCC halin da ake ciki tun farko
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, zai gurfana a gaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da misalin ƙarfe 10:00 na safiyar ranar Litinin mai zuwa.
Lauyansa, Ubong Esop Akpan, ne ya bayyana hakan yayin da yake mayar da martani kan yunƙurin kama El-Rufai a filin jirgin saman Abuja.

Source: Facebook
El-Rufai ya wallafa cikakkiyar sanarwar da lauyan ya fitar bayan abin da ya faru a filin jirgin sama a shafinsa na Facebook da yammacin yau Alhamis.
Yadda aka yi yunkurin kama El-Rufai
Ya ce jami’an tsaro sun tunkari El-Rufai ne da yammacin Alhamis bayan ya isa Abuja ta jirgin Egypt Air mai lamba MS 877 daga birnin Cairo na ƙasar Masar.
Akpan ya bayyana yunƙurin kama tsohon gwamnan a matsayin keta hakkin dan Adam da kundin tsarin mulki ya tanada, da kuma wuce gona da iri.
“Gayyatar da EFCC ta aike wa Malam El-Rufai ta iso ne yayin da yake ƙasar waje, wanda hakan ya sa ba zai yiwu a buƙaci ya amsa gayyatar nan take ba.
"Ba zai yiwu a yi tsammanin mutumin da ke wajen ƙasa ya kai kansa ofishin EFCC ba, ya riga ya yi tafiya, don haka ya kamata a masa adalci,” in ji shi.

Kara karanta wannan
Bidiyo: Yadda fasinjoji suka hana jami'an tsaro kama El Rufai a filin jirgin sama
El-Rufai zai gurfana a gaban EFCC
Lauyan ya ce tun watan Disamba na 2025 suka rubuta wa EFCC wasika don tabbatar da cewa El-Rufai zai amsa gayyatar da zarar ya dawo ƙasa.
Ya ƙara da cewa a ranar Laraba sun sake sanar da hukumar cewa tsohon gwamnan zai je ofishinsu da kansa da misalin ƙarfe 10:00 na safe ranar Litinin, 16 ga Fabrairu, 2026.
“Yunƙurin kama shi duk da wannan wasika da muka tura na nuna son rai da kuma tauye tsarin doka,” in ji Akpan.

Source: Twitter
Ya kuma ce babu wani dalili na doka da zai ba da hujjar yunƙurin kama shi, yana mai cewa hakan ya saba wa muhimman tanade-tanaden kundin tsarin mulki da ke kare ‘yancin dan Adam.
Akpan ya ce duk da sun samu bayanan sirri cewa ana shirin kama shi, El-Rufai ya dawo ƙasar bayan jinya da hutu a waje, yana mai bayyana shirinsa na fuskantar duk wani bincike na doka.

Kara karanta wannan
Jami'an tsaro sun ga takansu da suka yi yunkurin kama El Rufai a filin jirgin sama
El-Rufai ya yi hasashen za a kama shi
A wani rahoton, kun ji cewa tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa'i ya yi ikirarin cewa zai iya shiga hannun hukumomin Najeriya nan ba da jimawa ba.
El-Rufai fadi haka ne saboda yadda aka kama wasu daga cikin wadanda suka yi aiki da shi a lokacin da ya ke gwamna a Kaduna.
Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne a daidai lokacin da harkokin siyasa ke kara zafi yayin da ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.
Asali: Legit.ng
