Shiri Ya Baci: 'Yan Bindiga Sun Kashe 'Yan Sanda da Fararen Hula a Benue
- 'Yan bindiga dauke da makamai sun yi yunkurin kashe mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba a jihar Benue
- Tsagerun 'yan bindigan sun kai farmaki a wata kasuwa da ke kauyen Tse-Kaseve a karamar hukumar Katsina-Ala
- Jami'an tsaro sun yi artabu da su tare da fatattakarsu, an kashe 'yan sanda tare da wasu fararen hula hudu yayin harin
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Benue - 'Yan bindiga sun kashe jami'an 'yan sanda da wasu fararen hula yayin wani hari a jihar Benue.
'Yan bindigan sun kashe ’yan sanda biyu da fararen hula hudu yayin wani harin da suka kai a kauyen Tse-Kaseve da ke gundumar Anyagba, a karamar hukumar Katsina-Ala ta jihar Benue.

Source: Facebook
Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan
Hankula sun tashi bayan 'yan bindiga sun farmaki jami'an tsaro a Katsina, an yi kisa
'Yan bindiga sun kashe 'yan sanda
Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne ranar Litinin, 9 ga watan Fabrairun 2026 da misalin ƙarfe 4:00 na yamma.
An bayyana cewa ’yan bindigan dauke da makamai sun mamaye yankin ne a kan babura kusan 100.
Majiyoyin sun ce maharan sun yi kokarin mamaye kasuwar kauyen domin kashe mazauna mutane, inda dakarun hadin gwiwa na jami’an tsaro suka fafata da su.
“Jami’an rundunar ’yan sanda ta tafi-da-gidanka (PMF) da ke aiki na musamman a garin, tare da haɗin gwiwar dakarun tsaro na sa-kai na jihar Benuwai, sun yi artabu da maharan tare da fatattakar su."
- Wata majiya
An kashe fararen hula
Sai dai yayin artabun, ’yan bindigan sun yi wa jami’ai biyu kwanton bauna, Sufeta Adams Saidu da Sufeta Edem Endimon, inda suka harbe su har lahira sannan suka tafi da bindigogin aikinsu.
Rundunar ta ce an kuma kashe fararen hula hudu a harin, yayin da wani mutum daya ya samu raunuka kuma aka garzaya da shi babban asibitin Katsina-Ala domin yi masa magani.
Bayan faruwar lamarin, an tura dakarun sojojin Najeriya tare da karin wasu tawagogin jami’an tsaro na musamman da ’yan banga zuwa yankin.
“Ana ci gaba da bincike a cikin daji domin kamo wadanda ake zargi da kai harin tare da kama su."
- Wata majiya

Source: Original
Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga
- Ana wata sai ga wata: 'Yan bindiga sun sake kai hari coci, sun sace masu ibada
- 'Yan bindiga sun yi kisa yayin da suka sace limami, ladan da wasu mutane
- Kanin Ado Aliero ya kai hari Katsina, sojoji sun gwabza fada da 'yan bindiga
'Yan bindiga sun farmaki jami'an tsaro
A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin kwanton bauna kan jami'an tsaro a jihar Katsina.
'Yan bindigan sun hallaka jami'in tsaro na rundunar C-Watch tare da jikkata wani bayan sun kai harin musu kwanton ɓauna a ƙaramar hukumar Musawa.
Tsagerun sun hallaka wani jami'i daya na rundunar tsaron (C-Watch), tare da jikkkata wasu jami'ai bayan harbinsu da bindiga.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
