Kotun Daukaka Kara Ta Raba Gardama kan Dakatarwar da Majalisa Ta Yi Wa Sanata Natasha

Kotun Daukaka Kara Ta Raba Gardama kan Dakatarwar da Majalisa Ta Yi Wa Sanata Natasha

  • Kotun daukaka kara ta zartar da hukunci a shari'ar da ke gabanta kan dakatarwar da majalisar dattawa ta yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan
  • A hukuncin da kotun ta yanke, ta bayyana cewa shugaban majalisar dattawa na da ikon ba 'yan majalisa wuraren zama ta hanyar ba su kujeru
  • Kotun ta bayyana cewa shugaban majalisar dattawa bai yi kuskure ba wajen hana Sanata Natasha yin magana yayin zaman majalisar na ranar, 20 ga watan Fabrairun 2025

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Kotun daukaka kara ta Abuja ta yanke hukunci kan dakatarwar da majalisar dattawa ta yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Kotun ta yi hukuncin cewa majalisar dattawa ta yi aiki ne a cikin ikon da doka ta ba ta lokacin da ta dakatar da sanatar mai wakiltar Kogi Ta Tsakiya, bisa zargin rashin da’a.

Kara karanta wannan

Matar Bola Tinubu ta yi mamakin abin da Shugaba Trump ya mata a taron jama'a a Amurka

Kotun daukaka ta yi hukunci a shari'ar Natasha
Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan Hoto: Natasha H Akpoti
Source: Facebook

Tashar Channels tv ta kawo rahoto cewa kotun daukaka karar ta yanke hukuncin ne a ranar Litinin, 9 ga watan Fabrairun 2026.

Kotun daukaka karar, a hukuncin bai daya da kwamitin alkalai uku ya yanke, ta ce ta gamsu cewa ba a take hakkin majalisa ko hakkin kundin tsarin mulki na sanatar ba sakamakon dakatarwar da aka yi mata daga majalisar dattawa.

Sai dai kotun ta soke tarar Naira miliyan 5 da aka yi mata dangane da saƙon neman afuwa na barkwanci da ta yi wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.

A cikin babban hukuncin da mai shari’a Abba Muhammed ya karanta, kotun ta bayyana cewa shugaban majalisar dattawa bai yi kuskure ba wajen hana Sanatar Kogi damar magana a zaman majalisa na ranar 20 ga Fabrairu, 2025.

Ya ce bai yi kuskure ba ne kasancewar ba ta zauna a kujerar hukuma da aka ware mata ba a lokacin zaman na majalisar dattawa.

Kara karanta wannan

Harin Kwara: Kungiyar CAN ta tura muhimmin sako ga Musulmi da aka hallaka

Kotun ta ƙara da cewa, dokokin Majalisar Dattawa sun bai wa shugaban majalisar ikon ware kujeru ga ‘yan majalisa, kuma doka ta tanadi cewa ɗan majalisa na da damar magana ne kawai daga kujerar da aka ware masa.

A cikin hukuncinta na ranar 4 ga Yuli, alkalin babbar kotu, Binta Nyako, ta yanke cewa hakkin da dan majalisa ke da shi yana karkashin tanadin dokokin majalisar dattawa.

Ta bayyana cewa shugaban majalisar dattawa yana da ikon sauya tsarin zama na sanatoci, tare da kara wa da cewa Godswill Akpabio ya yi daidai wajen hana Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan damar yin magana a zaman majalisa.

Sai dai kotun ta soki tsawon lokacin dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha, tana mai bayyana shi a matsayin “ya wuce gona da iri” kuma “ya yi tsanani fiye da kima.”

Haka kuma, kotun ta umarce ta da ta biya tarar Naira miliyan 5.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng