Yadda Ƴan Ta'adda Suka Rubuta wa Sarki Wasiƙu kan Shirin Hari kafin Hallaka Musulmai

Yadda Ƴan Ta'adda Suka Rubuta wa Sarki Wasiƙu kan Shirin Hari kafin Hallaka Musulmai

  • ‘Yan ta’adda sun aika wasiƙa ga al’ummar Nuru da Woro a Kwara, suna sanar da niyyarsu ta wa’azi kafin kai hari mai muni
  • Akalla mutane kusan 200 sun mutu, gidaje da dama sun ƙone, yayin da gwamnan Kwara ya danganta harin da tsattsauran ra’ayin addini
  • Basarake ya ce an sace iyalansa, yara biyu suka mutu, inda ‘yan ta’addan suka bukaci jama’a su guji gwamnatin Najeriya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kwara - Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan ta’adda sun rubuta wasiƙa ga mazauna Nuru da Woro a jihar Kwara, suna bayyana shirin wa’azi kafin kai hari.

A ranar Laraba 4 ga watan Fabrairun 2026, akalla mutane 200 ne suka rasa rayukansu, yayin da aka kona gidaje da dama lokacin harin da aka kai a karamar hukumar Kaiama.

Kara karanta wannan

Tinubu ya tura Shettima Kwara da muhimmin sako bayan kisan Musulmai

Yadda yan ta'adda suka yaudari Musulmi a Kwara kafin hallaka su
Dandazon Musulmi a Kwara yayin jana'izar yan uwansu da aka hallaka. Hoto: Reuters, BBC.
Source: Facebook

Gwamnatin Kwara ta gano dalilin hari a jihar

Gwamnan Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya danganta hare-haren da ‘yan tsattsauran ra’ayin addinin Musulunci da ke kokarin tayar da tarzoma, cewar TheCable.

Shugaba Bola Tinubu daga bisani ya bayar da umarnin tura rundunar sojoji ta bataliya zuwa yankin domin magance barazanar tsaro.

Har ila yau, Gwamna Abdul Rahman AbdulRazaq na Kwarai ya niki gari zuwa fadar shugaban kasa inda ya gana da Bola Tinubu domin neman mafita.

Yan ta'adda sun hallaka Musulmi 200 a Kwara
Taswirar jihar Kwara da yan ta'adda suka hallaka Musulmi 200. Hoto: Legit.
Source: Original

Wasikar da Sarki ya samu daga yan ta'adda

BBC ta ruwaito cewa ‘yan ta’addan sun aike da wasiƙa ga Sarkin Woro, Umar Bio Salihu, suna sanar da shi manufarsu.

An ce koyarwarsu tana da alaƙa da tsattsauran ra’ayi, wanda ya saba da fahimtar addinin Musulunci da yawancin mazauna yankin ke bi.

Salihu, wanda ba ya gida lokacin harin, ya ce ‘yan ta’addan sun fara zuwa gidansa inda suka sace matarsa da ’ya’yansa.

Kara karanta wannan

An fadi wadanda suka taimaka aka zubar da jinin Musulmai kusan 200 a Kwara

Abin da basaraken ya tarar a gidansa

Da ya dawo, ya tarar da gidansa ya ƙone kurmus, tare da gano gawarwakin yara biyu daga cikin ‘ya’yansa da aka kashe.

Ya ce ‘yan ta’addan sun bukaci al’umma su guji gwamnatin Najeriya su bi koyarwarsu, yana mai cewa hakan ya saba da koyarwar Alkur’ani.

Wani mazaunin Woro, Abdulla Umar Usman, ya ce ‘yan ta’addan sun shigo ƙauyukan da yawa, suna kai farmaki ba tare da tausayi ba.

Ya ce an kashe 'ya’yan basaraken biyu wadanda dalibai ne a bangaren likitanci a gaban gidansu kafin ‘yan ta’addan su banka masa wuta.

Lamarin ba a cewa komai - Mazaunin Kaiama

Wani malami da yake zaune a garin Kaiama, inda 'yan ta'addan suka yi wannan barna ya bayyana cewa ta'adin da suka gani ya yi muni ainun.

Ba tare da ya bari an kama sunansa ba, malamin makarantar ya shaida wa Legit Hausa cewa adadin wadanda aka hallaka za su iya zarce 200.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya firgita mutanen Abba Kabir bayan tara dandazon jama'a a Kano

A cewarsa, jami'an tsaro sun yi nasarar fara kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a kashe mutane a kauyukan na Kaima a makon nan.

Yaron Shekau ya kashe Musulmi a Kwara

Mun ba ku labarin cewa majiyoyi sun gano cewa kisan gillar da aka yi wa Musumai kusan 200 a Woro da ke karamar hukumar Kaiama ta Kwara na da alaƙa da tsattsauran ra'ayi.

Rahotanni sun danganta harin da Abubakar Saidu, wanda aka fi sani da Sadiku, wani babban dan ta'adda da ke da alaka da Abubakar Shekau.

Masana tsaro sun ce kwararan shaidu na nuna yadda yankin Kainji ya zama sabuwar mafakar ‘yan ta’adda a Arewa ta Tsakiyan Najeriya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.