Mutane Sun Fusata, Sun Bankawa Wani Matashi Wuta a Jihar Kano

Mutane Sun Fusata, Sun Bankawa Wani Matashi Wuta a Jihar Kano

  • An kama matashi da ake zargin barawo ne bayan ya yi kokarin kwace wayar wata mata a Dorayi Karshen Waya a cikin birnin Kano
  • Matasa sun fusata saboda yadda barayon ya nemi hallaka matar, sun lakada masa dukan tsiya sannan suka banka masa wuta
  • Rahotanni sun nuna cewa jami'an tsaro sun kai dauki wurin daga baya, sun tafi da wanda ake zargin domin ci gaba da bincike

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Yayain da ake ci gaba da jimamin kisan matar aure, Fatima da yaranta shida, matasa sun fusata da aka kama wani matashi da laifin yunkurin satar wayar salula a Kano.

Rahotanni sun nuna cewa matasa sun banka wa matashin da ake zargi da satar waya wuta a unguwar Dorayi, yankin Karshen Waya da ke jihar Kano.

Kara karanta wannan

Barawon motar Naira miliyan 75 ya yi wa 'yan sanda barkwanci a Kano

Jihar Kano.
Taswirar jihar Kano a Arewacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

An kama barawon waya a Dorayi

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa an kama barawon ne bayan ya yi yunkurin kwace wa wata mata wayar salula, amma dai bai samu nasara ba.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne bayan wanda ake zargin ya farmaki matar, inda ya daba mata wuka a kirji.

Wannan danyen aiki ya tunzura mazauna unguwar Dirayi, musamman matasa, wadanda suka kama wanda ake zargin suka yi masa dukan tsiya sannan suka kone shi.

Barawo ya illata wata mata a Kano

Bayanai daga mazauna Dorayi sun nuna cewa an gaggauta kai matar da aka raunata zuwa asibiti mafi kusa domin ba ta kulawar gaggawa.

A gefe guda kuma, jami’an tsaro sun isa wurin daga baya inda suka tafi da wanda ake zargin domin ci gaba da bincike.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, rundunar ’yan sandan jihar Kano ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

Kara karanta wannan

Wasu kwamishinoni sun rikita gwamnatin Kano bayan komawar Abba APC? Gaskiya ta fito

Rundunar yan sanda ta yi shiru

Haka kuma, duk wani yunkuri na jin ta bakin jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, bai kai ga nasara ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Jihar Kano dai na fama da irin wadannan matsaloli na satar waya, inda 'yan daba ke amfani da makami wajen kwace muhimman abubuwa daga hannun mutane.

Kakakin yan sandan Kano.
Jami'in hulda da jama'a na rundunar yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Source: Facebook

'Yan daban na iya kashe mutum don kawai su kwace wayarsa, to sai dai gwamnatin Kano da rundunar 'yan sanda sun dauki matakai, wadanda suka kawo saukin matsalar.

Matasan Dorayi sun rufarwa barawon musamman bayan yadda ya nemi kashe matar domin karbe wayarsa, daga bisani suka banka masa wuta, kamar yadda Aminiya ta kawo.

An kashe matar aure da yaranta 6 a Kano

A wani labarin, kun ji cewa waua tsageru sun haura har cikin gida, sun kashe matar aure da yaranta shida a unguwar Dirayi Chiranci a cikin birnin Kano.

Kara karanta wannan

Jirgin sama dauke da fasinjoji ya gamu da tsautsayi, 'dan Majalisa da mutane 14 sun mutu

Mazauna unguwar Dorayi Chiranci sun shiga tsahin hankali da firgici bayan kisan rashin imani da aka yi wa wata matar mai suna Fatima da 'ya'yanta.

Mutanen yankin sun bayyana lamarin a matsayin abin firgici da ban tsoro, wanda ba a taɓa ganin irinsa ba, inda suka nuna alhini da fargaba kan asarar rayukan da aka yi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262