Masu Safarar Makamai ga Tantirin Jagoran 'Yan Bindiga Sun Shiga Hannun Jami'an Tsaro
- Jami'an tsaro sun samu nasarar yin caraf da wasu mutane da ke safarar makamai a jihar Sokoto da ke yankin Arewa maso Yammacin Najeriya
- Mutanen dai an cafke su ne lokacin da suke yunkurin karbo makamai domin kai wa ga tantirin jagoran 'yan bindiga a jihar Zamfara
- Majiyoyi sun bayyana yadda jami'an tsaron suka samu nasarar cafke mutanen da ake zargi wadanda suke tafiya a kan babura
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Sokoto - Jami’an tsaro a jihar Sokoto sun cafke wasu mutane biyu da ake zargin masu safarar makamai ne.
Jami'an tsaron sun cafke mutanen ne yayin da suke kokarin kai makamai zuwa hannun wani fitaccen jagoran ‘yan bindiga a jihar Zamfara.

Source: Twitter
Masani kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan
An 'gano' wani shiri da masu juyin mulki suka yi domin hana Buhari ba Tinubu mulki
Yadda aka cafke masu kai wa Baleri makamai
Wata majiya ta ce a ranar 27 ga Janairun 2026, da misalin karfe 10:00 na dare, jami’an PMF 7 da ke gudanar da aikin bincike na yau da kullum a Bimasa da ke karamar hukumar Tureta, sun tare wasu mutane.
Jami'an tsaron dai sun dakatar da mutanen guda biyu da ke kan babura bayan da suka nuna alamun shakku.
An bayyana sunayen wadanda ake zargin da Alkamatu Nasiru da Shahidu Ibrahim, dukansu ‘yan kauyen Yan Matankari ne a karamar hukumar Anka ta jihar Zamfara.
Masu safarar makamai sun shiga hannu
Bayan bincike, an same su sanye da rigunan kariya masu kama da na sojoji a karkashin kayan jikinsu, tare da wukake biyu a hannunsu.
“Wadanda ake zargin sun amsa cewa suna kan hanyarsu ta karbar bindigogin AK-47 ne domin kai su ga Abdul Baleri, wani sanannen jagoran ‘yan bindiga da ke aikata ta’addanci a jihar Zamfara."
- Wata majiya
A halin yanzu, ana ci gaba da bincike domin gano tushen makaman, tare da bankado sauran mutanen da ke da hannu a haramtacciyar harkar safarar makamai.

Source: Original
Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga
- Jita jita ta kare: Babban alkalin Katsina ya tsage gaskiya kan batun sakin 'yan bindiga 70
- Yadda aka kama kayan hada bama bamai masu yawa za a kai wa ƴan bindiga a Zamfara
- Jami'an tsaro sun gwabza fada da 'yan bindiga a Gombe, an kashe 'yan ta'adda
'Yan bindiga sun kafa sharudda a Kaduna
A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga sun kafa sharuddan da suke so a cika musu kafin su saki masu ibada a coci da suka yi garkuwa da su a jihar Kaduna.
Mai unguwar kauyen da lamarin ya auku, ya bayyana cewa ’yan bindigan da suka sace kusan masu ibada 177 sun buƙaci a biya Naira miliyan 250 tare da babura 20 domin sakin su.
Jami'an tsaro sun gano inda aka kai mutanen da aka sace, amma ’yan bindigan na amfani da su a matsayin garkuwa domin hana kai hare-haren sama kan sansaninsu.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
