Bayan Manoma Sun Tafka Asara a Arewa, An ba Gwamnatin Tinubu Shawara kan Shigo da Shinkafa

Bayan Manoma Sun Tafka Asara a Arewa, An ba Gwamnatin Tinubu Shawara kan Shigo da Shinkafa

  • An fara neman gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dakatar da shigo da shinkafa daga kasashen ketare
  • Wani kwamitin manufofin noma da ke samun goyon bayan fadar shugaban kasa ya nuna damuwarsa kan adadin shinkafar da ke cikin Najeriya
  • Ya ce alkaluman kasuwannin duniya sun nuna cewa 'yan Najeriya sun shigo da shinkafa sama da tan miliyan 2 kan makudan kudade

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Wani kwamitin tsara manufofin harkar noma da gwamnatin tarayya ke marawa baya ya ba da shawarar rufe dukkan kofofin shigo da shinkafa a hukumance.

Kwamitin ya dogara ne da raguwar hauhawar farashin abinci da hujjojin da ke nuna cewa yawaitar shinkafa a Najeriya ta samo asali ne daga yawan shigo da ita daga waje, ba a gida aka noma ta ba.

Kara karanta wannan

Jerin manyan sojoji 16 da hedkwatar tsaro 'ta gano' suna da hannu a shirin kifar da Tinubu

Shinkafa.
Shinkafa yar gwamnati a wurin yan kasuwa a Najeriya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Wannan shawara na zuwa ne a lokacin da 'yan Najeriya suka kashe sama da N1tn wajen shigo da tan miliyan 2.4 na shinkafa cikin kasar, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Haka zalika, manoman shinkafa sun tafka asara a bana saboda yawna shigo da ita daga waje, wanda ya jawo faduwar farashi saboda yawan da ta yi a kasuwanni.

Yadda shigo da shinkafa ya wuce gona da iri

Idan aka duba alkaluman kasuwannin duniya, yawan shinkafar da aka shigo da ita Najeriya a 2025 ya nuna yadda aka fitar da makudan kudaden ketare, kodayake alkaluman kiyasi ne kawai.

Bisa farashin Thailand, kowane tan guda na shinkafa na kai wa kusan $370, wanda hakan na nuna cewa tan miliyan 2.4 zai ci Dalar Amurka miliyan 888, wanda ya yi daidai da kusan N1.26tn a farashin canji na babban bankin Najeriya.

Farashin shinkafar Indiya kuma ya fi sauki, kowane tan na kai wa kusan $347, wanda zai sa kudin ya koma kusan Dalar Amurka miliyan 832.8, kwatankwacin N1.18tn.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu 'ya amince' da kirkiro sabuwar jiha 1 a Najeriya, an bayyana sunanta

An nemi a dakatar da shigo da shinkafa

Biyo bayan shigo da tan miliyan 2.4, kwamitin ya ba da shawarar cewa gwamnatin tarayya ta rufe bodar shigo da shinkafa "ganin cewa hauhawar farashin abinci ya fadi kasa da kashi 14%."

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar bayan taro na biyu na tsarin National Agribusiness Policy Mechanism (NAPM) da aka gudanar a Abuja a watan Disambar 2025, in ji rahoton Bussiness Day.

Shugaban Tinubu.
Shinkafa yar gwamnati da Shugaba Bola Ahmed Tinubu Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

An kaddamar da wannan tsarin ne a watan Mayun 2025 domin hada kan manufofin abinci da noma na Najeriya ta hanyar amfani da sahihan bayanai. Kwamitin kula da harkokin abinci na shugaban kasa, ke kula da wannan tsari.

"Najeriya na da isasshen abinci, amma wadatar abinci musamman shinkafa da alkama har yanzu ya dogara ne kan shigo da su, wanda hakan ke nuna nakasu a tsarin noma na cikin gida," in ji sanarwar.

Farashin abinci ya sauka a Abuja

A wani labarin, kun ji cewa farashin wasu muhimman kayan abinci da ake amfani da su yau da kullum ya sake sauka a kasuwannin Babban Birnin Tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

Ta tabbata an yi yunkurin yi wa Tinubu juyin mulki, sojojin Najeriya sun fitar da bayanai

Binciken kasuwa da aka yi ya nuna cewa bayan bukukuwan Kirsimeti, farashin kayan abinci kamar tumatir, barkono, albasa, dankali da wake ya ragu a yawancin kasuwanni.

Wasu mazauna yankin sun ce raguwar farashin ta kawo musu sauƙi, amma sun bukaci gwamnati ta tabbatar da dorewar lamarin, ganin yadda ƙarfin sayen jama’a ke ƙara raguwa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262