'Yan Ta'adda Sun Take Yarjejeniyar Sulhu, Sun Afkawa Katsinawa

'Yan Ta'adda Sun Take Yarjejeniyar Sulhu, Sun Afkawa Katsinawa

  • Wasu 'yan ta'adda sun sake kai hari garin Dandume a jihar Katsina duk da yarjejeniyar zaman lafiya da aka kulla a kwanakin baya
  • A wannan hari da suka kai, jami’an tsaro sun dakile shi cikin gaggawa wanda ya ceci rayukan bayin Allah da ke zaune a yankin
  • Sai dai bayan an kora su daga Dandume, ‘yan bindigan sun kai mummunan hari Chibauna a Funtua, duka a cikin jihar Katsina

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Kara karanta wannan

Jami'an tsaro sun gwabza fada da 'yan bindiga a Gombe, an kashe 'yan ta'adda

Jihar Kano – Sabuwar matsala ta afkawa yankin Dandume da ke Karamar Hukumar Dandume a Jihar Katsina a daren Litinin, 25 ga watan Janairu, 2026.

Rahotanni daga mazauna yankin sun bayyana cewa jami’an tsaro sun kai dauki cikin hanzari, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa ba tare da sun yi mummunar barna ba.

'Yan ta'adda sun kai hare-hare jihar Katsina
Sufeton yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun Hoto: Nigeria Police Force
Source: Facebook

Bakatsine ya wallafa a shafin X cewa abin da aka tabbatar shi ne sace babur guda daya kacal a yayin artabun.

Yadda sojoji suka dakile harin 'yan ta'adda

Sojojin kasar nan sun samu nasarar dakile harin da 'yan ta'adda suka kitsa kai wa Dandume bayan samun bayanan sirri.

A sakon da Bakatsine ya wallafa, ya ce:

“Martanin gaggawa da jami’an tsaro suka yi a Dandume ya hana faruwar abin da zai iya zama bala’i. Wannan ya nuna muhimmancin bayanan sirri da hadin kai da al’umma.”

Sai dai duk da wannan nasara, wasu mazauna Dandume sun shaida cewa har yanzu mutane na cikin fargaba, suna kwana cikin shiri.

Yan ta'addan Katsina sun karya yarjejeniyar sulhu
Wasu daga cikin yan ta'addan da suka addabi Katsinawa Hoto: @ZagazOlaMakama
Source: Twitter

Sun kara da kira ga gwamnati da ta kara tsaurara matakan tsaro musamman a hanyoyin da ke hada kananan hukumomi.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun sake kai hari a Katsina, an kashe jami'an tsaro

Wasu 'yan ta'adda sun afkawa gari a Katsina

Bayan ficewar 'yan ta'addan daga Dandume, rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun sake haduwa tare da kai hari a kauyen Chibauna da ke Karamar Hukumar Funtua.

A nan ne aka ruwaito kisan fararen hula, sace wasu da dama, da kuma wawashe dukiyoyin jama’a.

Wannan lamari ya sake tayar da hankalin al’umma, musamman ganin cewa yankin na daga cikin wuraren da aka taba kulla yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindiga.

Majiyar ta kara da cewa:

“Abin tambaya yanzu shi ne: ta ya ‘yan bindiga ke yawo daga Karamar Hukuma zuwa wata ba tare da shinge ba? Kuma ina yarjejeniyoyin zaman lafiya suka dosa?”

'Yan ta'adda sun karya yarjejeniya a Katsina

A baya, mun wallafa cewa akalla mutane takwas ne suka rasa rayukansu bayan wasu ‘yan bindiga sun kai munanan hare-hare a wasu kauyuka a Dandume da ke Katsina.

Rahotanni sun nuna cewa harin ya faru ne da daren ranar Laraba, 21 ga watan Janairu, 2026, lokacin da yawancin jama’a ke shirin kwanciya barci

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa maharan sun shiga kauyukan ne cikin duhun dare, suna harbi ba tare da nuna tausayi ba, hakan ya jefa jama’a cikin mummunar firgici.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng