El Rufai Ya Saka Ayar Tambaya kan Yadda Ake Yaki da Cin Hanci da Rashawa a Najeriya

El Rufai Ya Saka Ayar Tambaya kan Yadda Ake Yaki da Cin Hanci da Rashawa a Najeriya

  • Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya yi tsokaci kan yadda ake yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya
  • Nasir El-Rufai ya zargi gwamnatin Najeriya da tafiyar da harkokin kasa ba tare da bin ka'ida ba, inda ya ce hakan na ds illa sosai
  • Hakazalika, tsohon gwamnan ya bayyana cewa mutanen da ke bangaren adawa sun fi fuskantar barazana wajen yaki da cin hanci da rashawa

​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya zargi gwamnatin Najeriya da tafiyar da ƙasa ba tare da bin ka'ida ba.

Malam Nasir El-Rufai ya bayyana cewa ana gudanar da mulki ne ba tare da ɗaukar alhakin ayyuka yadda ya kamata ba.

El-Rufai ya nuna shakku kan yaki da cin hanci da rashawa
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai Hoto: @elrufai
Source: Twitter

Nasir El-Rufai ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron muhawarar Daily Trust karo na 23, wanda aka gudanar ranar Alhamis, 22 ga watan Janairun 2026 a birnin tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

Binciken makamai: Malami na tsaka mai wuya a hannun hukumar DSS, ya fito ya yi magana

Nasir El-Rufai ya koka kan yaki da cin hanci

El-Rufai ya yi gargaɗi kan abin da ya kira son kai wajen yaƙi da cin hanci da rashawa, yana mai cewa wannan dabara na raunana dimokuraɗiyya, lalata gaskiya da kuma rage amincewar jama’a ga gwamnati.

Ya bukaci a kawo ƙarshen tsare mutane ba tare da cikakken bincike ba, yana mai gargadin cewa kama mutane babu hujja da tsare su na dogon lokaci ya zama ruwan dare.

Tsohon gwamnan na Kaduna ya kuma ce ana amfani da dabarar cafke mutane ne a matsayin hanyar tsoratarwa, ba don neman adalci ba.

El-Rufai ya nuna damuwa kan abin da ya bayyana a matsayin son kai wajen gurfanarwa, musamman ga mutanen da ake ganin suna sukar gwamnati ko kuma adawa da ita.

Ya ce irin waɗannan ayyuka suna take ’yancin ɗan Adam na kuma suna raunana tubalin dimokuraɗiyya a hankali.

El-Rufai ya yi zargi kan gwamnatin Najeriya

Tsohon gwamnan ya kuma zargi gwamnati da kare masu cin hanci da rashawa da ke cikin masu mulki, yana mai bayyana halin da ake ciki a matsayin “mulki ba tare da bin ka'ida ba".

Kara karanta wannan

Abubakar Malami ya yi magana game da makamai da DSS ta gano a 'gidansa' na Kebbi

Ya ce yawanci ana bin zargin cin hanci da tsanani ne ga ’yan adawa, yayin da waɗanda ke kusa da mulki ake watsi da su ko kuma a bar su, su sasanta kansu ta hanya daban.

A cewarsa, ba a tuhumar 'yan APC da rashin gaskiya sannan ana amfani da yakin wajen muzguna wa 'yan adawa da kuma kokarin jawo mutane sun shigo jam'iyya mai-ci.

“Ana tafiyar da mulki ba tare da bin ka'ida ba. Muna gudanar da zaɓe, muna kafa hukumomi, muna sanar da kwato kadarori, amma daftarin mulki yana ci gaba da kasancewa abin da ake jingina da shi ne kawai."
"Cin hanci ya zama abu mai haɗari ga wasu da ke cikin adawa, abin tattaunawa ga waɗanda ke tsaka-tsaki kuma suke son komawa APC. Ba a zargin 'yan APC da cin hanci.”

- Nasir El-Rufai

El-Rufai ya yi zargi kan gwamnatin Najeriya
Nasir El-Rufai a wajen taron jam'iyyar ADC Hoto: @elrufai
Source: Twitter

Tsohon gwamnan Kaduna ya ba da shawara

Ya yi kira ga shugabannin siyasa, kungiyoyin fararen hula da al’umma gaba ɗaya da su matsa lamba domin a aiwatar da gyare-gyare.

El-Rufai ya ce kawo karshen tsare mutane ba tare da bincike ba da kuma aiwatar da dokokin yaƙi da cin hanci ba tare da nuna bambanci ba, wajibi ne ta fuskar doka.

Kara karanta wannan

Atiku ya yi magana kan sace masu ibada a Kaduna, ya fadi kuskuren gwamnati

A 'yan kwanakin nan an ji yadda EFCC da DSS suka tsare Abubakar Malami wanda ya yi minista na kusan shekaru takwas a mulkin Muhammadu Buhari.

El-Rufai ya yabi gwamnatin Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yabawa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

El-Rufa'i ya yi yabon ne bisa matakin da gwamnatin tarayya ta ɗauka kan yaƙi da garkuwa da mutane, na kin ba da kudin fansa.

Tsohon gwamnan ya bayyana cewa ya kamata a karfafa wa gwamnati gwiwa a kan wannan mataki, domin hakan zai taimaka wa Najeriya wajen yaki da tsaro.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng