Kano: Yadda Ake Kyamatar Yan Uwan Fatima da Aka Yi wa Kisan Gilla a Zaman Makoki

Kano: Yadda Ake Kyamatar Yan Uwan Fatima da Aka Yi wa Kisan Gilla a Zaman Makoki

  • Wasu daga cikin ’yan uwan Fatima Abubakar da aka kashe tare da ’ya’yanta shida sun koka cewa ana nuna musu kyama yayin zaman makoki
  • Daya daga cikinsu ta ce dangin mijin marigayiyar na kyamar su, har ta kai an hana su gaisuwa, duk da cewa su ma mutuwar ta shafe su matuƙa
  • Ta bayyana cewa lamarin kisan gilla ya jefa su cikin baƙin ciki da kunci, tana cewa har yanzu suna jin zafi kuma ba sa samun kwanciyar hankali

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Wasu daga cikin yan uwan Fatima Abubakar da aka yi wa kisan gilla da 'ya'yanta shida sun koka kan halin da suke ciki.

Yan uwan matar da ta rasa ranta dalilin kisan gilla suka ce ana kyamarsu a gidan da ake zaman makoki duk da cewa su ma mutuwar ta shafe su.

Kara karanta wannan

Makwabtan Fatima da aka kashe da yaranta 6 a Kano sun fusata rundunar 'yan sanda

Yan uwan Fatima da aka hallaka da 'ya'yanta suna fuskantar kyama
Malam Haruna Bashir da iyalansa kafin yi musu kisan gilla. Hoto: Abba Hikima.
Source: Facebook

Yan uwan marigayiya Fatima sun koka

Daya daga cikin yan uwan, Sadiya Abubakar ya bayyana haka a faifan bidiyo da jaridar Freedom Radio ta wallafa a shafin Facebook.

Sadiya ta ce dangin mahafin yaran da aka hallaka suna nuna musu kyama musamman yayin zaman makoki da ake yi.

Ta ce sun je gaisuwa a unguwar amma ba su samu mijin marigayiyar ba, sai suka bukaci gaishe da babarsa amma aka hana su.

Ta ce:

"Tun da aka ce dan uwanmu ne ya yi wannan abu, sai ake ganin kamar daga jininmu ne, kamar ana nuna mana abu na rashin dadi.
"Da muka je kofar Nasarawa muka yi gaisuwa, to mijin bayanan, sai na ce to zan je wurin babarsa na yi mata gaisuwa sai aka ce a'a.
"In dawo ka da rai ya baci, sai na rasa ma'anar wannan magana, wato suna nufin daga dangin na mu ne, ba za mu so mu yi wannan abin ba."

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Mutum ɗauke da adda ya tarwatsa masu ibada, ya ce ana damunsa

Ana ci gaba da jajanta wa Haruna Bashir bayan yi wa iyalinsa kisan gilla
Malam Haruna Bashir da iyalansa kafin su yi bankwana da duniya. Hoto: Kwankwasiyya Trustworthy NG.
Source: Facebook

Kano: Halin da yan uwan Fatima ke ciki

Sadiya ta ce wallahi abin da ya faru yana taba su sosai kuma suna cikin kunci kan lamarin da ya faru na kashe-kashe da yaron ke yi.

Ta ce abin takaici ne yadda yar uwarsu ta rasa ranta a mummunan hali amma kuma ana kyamarsu saboda dan uwansu ne ya aikata haka.

"Mu ma ba a son ranmu wannan abin ya faru ba, 'dan yayanmu ne, ya kashe kanwar babarsa da kuma kanwarsa da aka kwakule mata ido.
"Mu dai wannan mutuwa da aka yi wallahi har yanzu muna jin zafin mutuwar nan, bacci ma idan ina yi maganganu na ke yi."

- Sadiya Abubakar

Kisa gilla: Sarki Sanusi ya roki Abba alfarma

Mun ba ku labarin cewa Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya yi jimamin kisan gilla da aka yi wa wata mata da 'ya'yanta shida wanda ya tayar da hankali.

Kara karanta wannan

Mutanen Dorayi sun fadi ainihin abin da ya faru kan kisan Fatima da yaranta 6 a Kano

Basaraken ya bukaci Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya rattaba hannu kan hukuncin kisa ga masu laifin kisan kai.

Sarkin ya ce rashin aiwatar da hukuncin kisa na kara bai wa masu aikata kisan gilla kwarin gwiwar ci gaba da aikata laifuffuka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.