Babbar Magana: An Gano Yadda Miliyoyi Suka Yi Batan Dabo a Mulkin Yahaya Bello

Babbar Magana: An Gano Yadda Miliyoyi Suka Yi Batan Dabo a Mulkin Yahaya Bello

  • Shaida a kotu ta bayyana yadda Hukumar Haraji ta Jihar Kogi ta rika tura makudan kudi zuwa wani kamfani mai zaman kansa
  • Shaidu sun ce an canja ma'ajiyar kudade sama da miliyan 57 zuwa 242 daga KSIRS zuwa wani kamfani daban
  • EFCC na tuhumar tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello, da karkatar da fiye da ₦110bn, duk da cewa ya musanta zargin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Wani jami’in banki ya shaida wa Babbar Kotun Abuja yadda wani kamfani mai zaman kansa ya karɓi manyan kudade daga Hukumar Haraji ta Jihar Kogi.

Shaidan, David Ajoma, jami’i a Sterling Bank, ya tabbatar da canja ma'ajiyar kudi guda shida daga KSIRS zuwa 'Bespoque Business Solutions Limited'.

Ana ci gaba da binciken kudade a mulkim Yahaya Bello
Tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello da mashigar hukumar EFCC. Hoto: Economic and Financial Crimes Commission.
Source: Twitter

An gano batan miliyoyi a mulkin Yahaya Bello

Ya ce wadannan kudade sun kai miliyoyi, kuma an tura su ne a lokacin da Yahaya Bello ke rike da mukamin gwamnan Jihar Kogi, cewar Premium Times.

Kara karanta wannan

EFCC ta bude wa tsohon gwamna Yahaya Bello aiki, ta kawo hujjoji a kansa a kotu

EFCC na gurfanar da Yahaya Bello tare da Umar Shuaibu Oricha da Abdulsalami Hudu kan zargin karkatar da kudaden gwamnatin jihar.

Hukumar ta ce Bello ya yi amfani da kudaden da ake zargi ya sace wajen sayen gidaje a manyan wurare a Abuja da kuma wani gida a Dubai.

Dukkan wadanda ake tuhuma sun musanta zargin, suna mai cewa ba su aikata laifin karkatar da kudin jama’a ba.

A gaban kotu, lauyan EFCC, Kemi Pinheiro SAN, ya gabatar da bayanan kudaden da aka dauka a matsayin masu matukar tayar da hankali.

Shaidar ta ce a ranar 5 ga Maris 2019, KSIRS ta tura sama da ₦57.9m zuwa asusun BBSL.

Haka kuma, a ranar 4 ga Afrilu 2019, an tura sama da ₦138m da bayanin “Kudin hukumar Kogi na watan Maris.”

An kuma tura ₦126.8m a ranar 3 ga Mayu 2019, sai ₦97m a ranar 6 ga Yuni 2019, kamar yadda TheCable ta ruwaito.

Badakalar kudade na ci gaba da fitowa a mulkin Yahaya Bello
Tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello. Hoto: Alhaji Yahaya Bello.
Source: Facebook

Yahaya Bello: An gabatar da shaidu a kotu

A watan Agustan 2019, BBSL ta karɓi ₦183.6m domin biyan ‘yan kwangila, sannan ₦242.2m domin sayen OPBEH.

Kara karanta wannan

Bayan kashe mutane fiye da 40, Gwamna Bago ya fadi dalilin 'yan bindiga na farmakar Kasuwan Daji

Bayan kammala shaidar, alkalin kotu ya dage sauraron shari’ar zuwa 16 ga Janairu domin ci gaba da sauraro.

Wani shaida daban ya ce ma’amalolin da aka yi daga KSIRS zuwa BBSL ba su da cikakken bayani kan manufarsu.

Shaidan ya kuma bayyana cewa sunan Yahaya Bello bai bayyana a matsayin wanda ya amfana kai tsaye daga wadannan kudade ba.

Sai dai ya ce sunan Abdulsalami Hudu ya bayyana sau da dama, inda aka bayyana shi ga banki a matsayin akawun jihar.

EFCC ta gabatar da hujjoji kan Yahaya Bello

Kun ji cewa Hukumar EFCC ta sake gabatar da wasu muhimman bayanan banki a gaban kotun tarayya kan shari’ar tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello.

Shari’ar na ɗauke da tuhume-tuhume 16 da suka shafi cin amana da karkatar da kudi da ake zargin Yahaya Bello da suka kai Naira biliyan 110.4.

Shaidar banki ta bayyana wasu manyan kuɗi da aka biya ta wani asusu, amma ba a nuna takamaiman manufar wasu mu’amaloli da ka yi da su ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.