Rashin Tsaro: Daruruwan Malaman Musulunci Sun Sauke Alkur’ani, Addu’o’i a Kano
- Limaman Najeriya sun fara taron addu’o’i a Kano domin neman taimakon Allah kan tabarbarewar tsaro da matsalolin siyasa da ke addabar ƙasar
- Taron ya haɗa limamai, shugabannin addini da dubban mabiya, inda aka yi saukar Alƙur’ani da addu’o’in neman zaman lafiya da kariya a ranar Alhamis
- Ƙungiyar ta ce za a faɗaɗa taron addu’ar zuwa dukkan jihohi 36, tana kiran ’yan Najeriya su haɗa kai wajen roƙon Allah
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Kano - Ƙungiyar Limaman Najeriya ta gudanar da taron addu’o’i a Kano domin roƙon Allah ya kawo ƙarshen matsalar tsaro da ake fama da shi a kasar.
Malaman sun kuma sauke Alkur'ani mai girma domin kawo karshen rikice-rikicen da ke damun ƙasar nan wanda ke jawo asarar rayuka da dukiyoyi.

Source: Facebook
An yi addu'o'i a Kano kan rashin tsaro

Kara karanta wannan
Zafin siyasa bai hana aiki: Abba ya fadi shirin gwamnati a kan matasa 50, 000 a Kano
An gudanar da taron a Masallacin Sheikh Ahmadu Tijjani, inda limamai da mabiya daga sassa daban-daban suka taru domin yin addu’a kan ƙalubalen tsaro da siyasa, cewar Aminiya.
Shugaban ƙungiyar, Sheikh Muhammad Nasir Adam ya koka game da halin da ake ciki a kasar musamman a yankin Arewacin Najeriya.
Shehin Malamin ya ce sun shirya taron addu'o'in ne bayan kungiyar ta yanke shawarar daukar matakin domin neman taimakon Allah musamman kan matsalar tsaro.
Shugaban ƙungiyar, Sheikh Muhammad Nasir Adam, ya ce:
“Mun taru a nan bisa shawarar ƙungiyarmu… domin neman taimakon Allah kan matsalar tsaro.”

Source: Original
Matsalolin da Najeriya ke fama da su
Sheikh Muhammad Nasir Adam ya bayyana cewa Najeriya na fama da Boko Haram, ’yan bindiga da masu garkuwa, yana mai cewa addu’a ita ce babban makamin al’umma a halin yanzu.
“Mun fahimci cewa addu’a ita ce zaɓi na ƙarshe kuma ita ce babbar makaminmu, da roƙon Allah ya kare ƙasar."
- Sheikh Nasir
Limamin ya ce Najeriya ƙasa ce mai albarka da mutane masu juriya, yana kira ga haɗin kai, tawali’u da yawan addu’a domin samar da zaman lafiya.
Ƙungiyar malaman ta buɗe ƙofa ga dukkan ’yan Najeriya, ba tare da la’akari da addini ko aƙida ba, su shiga wannan aiki na addu’a.
Ta kuma sanar da cewa taron da aka fara a Kano zai ci gaba da gudana a dukkan jihohi 36 na Najeriya domin neman taimakon Allah game da fama da rashin tsaro.
Kano: Malamai sun yi addu'o'i ga Tinubu, Barau
A wani labarin, kungiyar wasu limamai a jihar Kano ta shirya addu’o’i na musamman domin samun nasarar shugaban kasa, Bola Tinubu da Sanata Barau Jibrin.
Kungiyar ta kunshi malaman Musulunci inda suka yi karatun Alkur'ani mai girma saboda samun nasara a zaben 2027 mai zuwa.
Malaman sun yi addu'o'i ga Tinubu da Barau, suna roƙon zaman lafiya, cigaban tattalin arziki, da kwanciyar hankali a ƙasar baki daya.
Asali: Legit.ng
