Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Sabon Tsari, Masu Amfani da Banki Za Su Fara Biyan VAT

Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Sabon Tsari, Masu Amfani da Banki Za Su Fara Biyan VAT

  • Bankunan kasuwanci da kamfanonin hada-hadar kudi ta intanet irinsu Moniepoint za su fara karbar harajin VAT daga abokan hulda
  • Gwamnatin tarayya ce ta ba da umarnin fara cire harajin na kashi 7.5 na ladar aika kudi daga ranar Litinin, 19 ga watan Janairu, 2025
  • Za a rika cire wannan haraji ne a abin da bankuna ke dauka idan mutum ya tura kudi ko wata mu'amala ta intanet amma ba za a taba asalin kudin ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Daga ranar Litinin, 19 ga watan Janairu, 2026, daukacin bankunan kasuwanci da kamfanonin hada-hadar kudi na intanet za su fara cire harajin VAT na kashi 7.5 daga asusun 'yan Najeriya.

Wannan sanarwa ta fito ne ta hanyar sakonnin imel da wasu kamfanonin hada-hadar kudi irin su Moniepoint suka fara aikawa abokan cinikinsu a ranar Laraba.

Kara karanta wannan

An faɗi lokacin fara cire harajin VAT a asusun bankuna, masu POS sun shiga ciki

Harajin VAT.
Harajin VAT Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Jaridar Punch ta ce gwamnatin tarayya ta hannun Hukumar Karbar Haraji ta Kasa (NRS), ce ta ba da umarnin fara cire harajin daga kudin caji da bankuna ke dauka.

Wadanne hada-hadar kudi ne harajin zai shafa?

Harajin na VAT ba zai shafi ainihin kudin da mutum ya tura ba, sai dai zai hau kan kudin da banki ke cirewa wajen gudanar da wadannan ayyuka.

Kudin da za a dauki harajin VAT daga cikinsu sun hada da:

  • Cajin tura kudi ta waya.
  • Kudaden hada-hadar amfani da lambobin sirri (USSD).
  • Kudaden karbar sabon katin cirar kudi (ATM).

Misali: Idan banki yana cire N100 a matsayin cajin tura kudi, to za a kara cire kashi 7.5% na wannan N100 din (wato N7.50) a matsayin harajin VAT da za a tura wa gwamnati.

Abubuwan da harajin ba zai shafa ba

Sanarwar ta bayyana cewa har yanzu akwai ayyukan da aka amince ba za a cire musu harajin ba, wadanda suka hada da, kudin ruwa da kudin da mutum ya tara a asusun ajiya, cewar rahoton Sahara Reporters.

Kara karanta wannan

Cikin rashin imani, 'yan bindiga sun harbe 'matar sarki' mai shekara 75

A sakon da lamfanin Moniepoint ya tura wa wakilinmu, ya nanata cewa wannan mataki ba karin kudi ba ne daga bangarensu, face bin dokar kasa da ta wajabta musu karbar harajin da kuma mika shi ga hukumar NRS.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Wannan sabon tsari na daya daga cikin kokarin gwamnati na dunkule tsarin karbar haraji a harkar hada-hadar kudi ta intanet, domin fadada hanyoyin samun kudin shiga da nufin bunkasa tattalin arzikin zamani na Najeriya.

Idan za a iya tunawa, a watan Disamba ma bankuna sun sanar da abokan cinikinsu cewa za a ci gaba da cire kudin harajin Stamp Duty na N50 a duk lokacin da suka tura N10,000 ko fiye da hakan, sakamakon fara aikin sabuwar Dokar Haraji.

Wani matashi mai sana'ar POS da kamfanin Moniepoint, Muhammad Yusuf ya tabbatar wa Legit Hausa cewa ya samu sako kan shirin fara cire wannan haraji.

Ya ce Moniepoint sun turo masa sako ta wayar salula cewa daga ranar Litinin za su fara cire wannan haraji, inda ya koka cewa hakan zai kara wa talakawa nauyi.

"Eh an turo mini sako, sai dai zan jira naga yadda tsarin zai yi aikin sannan dole mu yi tunanin karawa mutane kudin aikinmu.

Kara karanta wannan

Akwai matsala: Gwamnatin tarayya ta gamu da cikas a shirin aiwatar da dokar haraji

"A gaskiya ya kamata gwamnati ta tausaya mana, tsare-tsaren da ake bullowa da su, suna nema su kashe mana kasuwa, yanzu nema ake a hana mutane amfani da banki gaba daya," in ji shi.

An yi gyara a dokokin harajin Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta bayyana cewa kananun sauye-sauyen da aka samu ba za su rage komai a sababbin dokokin haraji ba.

Shugaban kwamitin sake fasalin haraji na shugaban kasa, Taiwo Oyedele, ne ya bayyana hakan a wani taro da ya halarta a jihar Legas.

Ya bayyana cewa duk da hayaniyar da ake yi na cewa an sauya wasu abubuwa, wadancan sassa ba su da yawa kuma ba su taba muhimman batutuwan haraji da suka shafi al'umma ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262