Rigimar Iko: Olubadan Ya 'Kunyata' Sarki Mai Martaba a tsakiyar Taron Jama'a a Najeriya

Rigimar Iko: Olubadan Ya 'Kunyata' Sarki Mai Martaba a tsakiyar Taron Jama'a a Najeriya

  • An yi wata yar dirama a wurin wani taro da manyan sarakunan kasar Yarbawa biyu suka halarta a Ibadan, babban birnin jihar Oyo
  • Lamarin ya faru ne lokacin da Olubadan na kasar Ibadan ya iso wurin taron, ya zauna a wurin da aka tanadar masa kusa da Alaafin
  • Sarakunan gargajiya na Ibadan sun nuna fushinsu kan rashin girmamawar da Alaafin ya nunawa Olubadan a wurin taron

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ibadan, Nigeria - Sarkin Ibadan, Rashidi Ladoja (Olubadan na Ibadanland) da Alaafin na Oyo, Abimbola Owoade, sun sake haifar da ce-ce-ku-ce bayan abin da ya faru a wurin taron addini a Ibadan.

Rahotanni sun nuna cewa manyan sarakunan biyu na neman dawo da tsohuwar gaba da rikicin iko da ya dade yana faruwa tsakaninsu.

Alaafin da Olubadan.
Olubadan na kasar Ibadan, Oba Rashidi Ladoja lokacin da ya ki gaisawa da Alaafin a taron addu'a Hoto: Arabinrin Opeyemi
Source: Facebook

The Cable ta ruwaito cewa sarakunan biyu masu daraja a kasar Yarbawa sun halarci taron addinai na 2026 da aka gudanar a Grand Space, kusa da majalisar dokokin jihar Oyo.

Kara karanta wannan

"Ina ya shiga?" Peter Obi ya fito da damuwarsa game da yawan tafiye tafiyen Tinubu

Me ya faru tsakanin Olubadan da Alaafin?

Wani bidiyo da ya bazu sosai a kafafen sada zumunta kuma TVC News ta wallafa a Facebook, ya nuna Olubadan yana tafiya zuwa wurin zamansa kusa da Alaafin, wanda ya riga ya iso tun da wuri kuma yana zaune.

Yayin da Ladoja ke karasowa, Owoade ya miƙa masa hannu domin gaisuwa ba tare da ya mike tsaye don girmama shi ba, amma Olubadan ya ƙi amsawa, lamarin da ya sa Alaafin ya janye hannunsa.

Wannan lamari ya sake tayar da tsohuwar rigimar tarihi kan matsayi da fifiko tsakanin manyan kujerun gargajiya biyu na yankin Yarbawa.

Sarakunan Ibadan sun soki dabi'ar Alaafin

Da suke martani kan lamarin, sarakunan gargajiya na Ibadan sun soki abin da Alaafin ya yi, suna bayyana shi a matsayin rashin girmamawa ga Olubadan da kuma masarautar Ibadan.

A cikin wata sanarwa, sarakunan sun ce Ibadanland ba ta ƙarƙashin ikon Alaafin, inda suka ƙara da cewa miƙa wa Olubadan hannu yayin da Alaafin ke zaune cin mutunci ne.

Kara karanta wannan

Sanatan Najeriya ya gina danƙareren gida, talakawa sun masa rubdugu a intanet

Sun yi kira ga Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo da ya gargadi Alaafin kan abin da suka kira “halaye na rashin tarbiyya” da yake nuna wa sarakunan gargajiya na Ibadan.

Sarakuna sun yi barazanar daukar mataki

Sanarwar ta ce:

“Rashin girmamawar Alaafin ga Olubadan da babbar masarautar Ibadan ya wuce kima.
“Idan Gwamna Seyi Makinde bai gargade shi ba, ya bar mutane da suka hada da sarakuna da hakimai su yi maganinsa, to fa duk abin da ya faru kada Alaafin ya zargi kowa ya zargi kansa
Olubadan
Oba Rashidi Ladoja a wurin bikin rantsar da shi a matsayin Olubadan na kasar Ibadan Hoto: Seyi Makinde
Source: Twitter

Sun ce akwai bayanai da dama na abubuwan da suka faru a baya da suke kallon su a matsayin rashin ladabi ga sarakunan gargajiya na Ibadan, tare da gargaɗin cewa Ibadanland ba za ta ci gaba da jurewa ba.

Sun ƙara da cewa bai dace ba Alaafin ya zauna yana miƙa hannu domin gaishe da Olubadan mai shekaru 82 a cikin ƙasar Ibadan ba.

Abin da Olubadan ya fadawa 'yan siyasa

A baya, kun ji cewa Sarkin Ibadan a jihar Oyo, Olubadan na Ibadanlanda, Oba Rashidi Ladoja ya karbi bakuncin manyan yan siyasa a fadarsa.

Kara karanta wannan

Rikicin Rivers: Matakin da Tinubu ya dauka bayan alaka ta sake tsami tsakanin Wike da Fubara

Oba Ladoja, tsohon gwamnan Oyo, ya shaida masu cewa shi ba dan siyasa ba ne yanzu, yana mai jaddada cewa zai yi hidima ga jama’ar Ibadan da Najeriya baki ɗaya.

Ya tuna irin dangantakarsa da Atiku Abubakar a jam’iyyu daban-daban, yana cewa yanzu manufarsa ita ce tabbatar da adalci, da zaman lafiya ga al’ummarsa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262