Jirgin Sama daga Kasar Saudiyya Ya Gamu da Babbar Matsala yayin Sauka a Jihar Kano

Jirgin Sama daga Kasar Saudiyya Ya Gamu da Babbar Matsala yayin Sauka a Jihar Kano

  • Wasu musulmi da suka dawo daga aikin Umrah a Saudiyya sun gamu da cikas yayin sauka a filin jirgin Kano, an karkatar da su zuwa Abuja
  • Rahoto ya nuna cewa bayan jirgin saman ya sauka a Abuja, ya bar mutanen da ya dauko a ciki har na tsawon awanni biyar
  • Fasinjojin sun yi kira ga hukumomin NCAA da FAAN su taimaka su shiga tsakani domin suna bukatar fitowa daga jirgin saman

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Wasu musulmai da suka dawo daga Umrah a Saudiyya su gamu da tangarda yayin da jirgin da ya dauko su zai sauka a jihar Kano.

Rahoto ya nuna cewa rashin kyaun yanayi ya sa aka karkata da akalar jirgin sama zuwa Abuja maimakon sauka a Kano kamar yadda aka tsara masa.

Kara karanta wannan

Trump na barazana ga Najeriya, 'dan bindiga ya kashe Kiristoci a cocin Amurka

Jirgin sama.
Jirgin sama na kamfanin Saudi Arabian Airlines yana tafiya a sararin samaniya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Leadership ta ce fasinjojin da ke dawowa daga kasar Saudiyya sun makale na tsawon kusan awa biyar a cikin jirgin Saudi Arabian Airlines a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja,

Dalilin karkatar da jirgin sama zuwa Abuja

An tsara jirgin zai sauka a Filin Jirgin Sama na Mallam Aminu Kano (MAKIA) da ke Kano, amma aka karkatar da shi zuwa Abuja a matsayin matakin kariya bayan samun rahoton yanayin iska da hadari a Kano.

Rahotanni sun nuna cewa jirgin ya sauka a Abuja da misalin karfe 1:00 na rana a yau Asabar, amma fasinjojin suka ci gaba da zama a cikin jirgin na fiye da awa biyar ba tare da an bude su.

Abin da fasinjojin suka ce a Abuja

Wasu daga cikin fasinjojin sun shaida wa PRNigeria ta wayar tarho cewa an barsu a cikin jirgin ba tare da abinci, ruwa, ko cikakken bayani daga kamfanin jirgin ba, inda suka bayyana lamarin a matsayin rashin tausayi da cin zarafi.

Kara karanta wannan

Abin da Kwankwaso da Ganduje suka fadawa Abba ana batun shigarsa APC

“Mun fahimci dalilin karkatar da jirgin domin tsaro, amma rufe mu a jirgin na fiye da awa biyar ba tare da wani bayani ko kulawa ta asali ba, kuskure ne da ba za su dauka ba,” in ji wani fasinja.
Jirgin sama
Jirgin sama na kamfanin Saudiyya yayin da ya sauka a filin jirgi Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Fasinjojin sun kuma nuna damuwa kan lafiyar mutanen da ke cikin jirgin, musamman tsofaffin da sauran wadanda suka riga suka gaji sakamakon doguwar tafiya.

“Wasu daga cikin ’yan uwanmu suna rashin lafiya a halin yanzu a cikin jirgin. Gajiyar tafiya da wannan jinkiri mai tsawo tare da rashin taimako na kara jefa mutane cikin wahala. Abin takaici ne kuma wulakanci.”

Sun yi kira ga Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Najeriya (FAAN) da kuma Hukumar Kula da Harkokin Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA) da su gaggauta shiga tsakani, ta hanyar sauke su daga jirgin.

Jirgin sama ya yi hatsari a Owerri

A wani labarin, kun ji cewa wani karamin jirgin sama kirar Cessna 172 ya gamu da hatsari a filin jirgin Owerri bayan ya samu tangarda tun a sararin samaniya.

An ce jirgin ya yi hatsari ne a filin jirgin kasa da kasa na Sam Mbakwe da ke Owerri, jihar Imo, yayin da yake kokarin sauka.

Rahotanni sun nuna cewa jirgin ya tashi ne daga filin jirgin sama na Kaduna zuwa Port Harcourt , kafin matukan jirgin su sanar da cewa sun samu matsala

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262