Jami'an Tsaro Sun Fafata da 'Yan Bindiga, an Ceto Mutanen da Aka Sace a Zamfara

Jami'an Tsaro Sun Fafata da 'Yan Bindiga, an Ceto Mutanen da Aka Sace a Zamfara

  • 'Yan bindiga sun kutsa zuwa kauyen Dunfawa na karamar hukumar Moriki ta jihar Zamfara, inda suka yi awon gaba da bayin Allah da dama
  • Jami'an tsaro sun kai daukin gaggawa inda suka yi artabu da tsagerun 'yan bindigan, inda hakan ya tilasta musu tserewa zuwa cikin daji
  • Biyo bayan ragargazar 'yan bindigan da jami'an tsaron suka yi, an samu nasarar ceto dukkanin mutanen da aka yi garkuwa da su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Zamfara - An samu nasarar ceto dukkan mutane 20 da aka sace daga kauyen Dunfawa da ke yankin Moriki, a karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa an ceto mutanen ne bayan 'yan bindiga sun sace su.

An ceto mutanen da 'yan bindiga suka sace a Zamfara
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

'Mutane sun fara guduwa,' Halin da ake ciki a Neja bayan kashe fiye da mutum 40

An sace mutanen ne tun da sanyin safiyar ranar Asabar, 3 ga watan Janairun 2026 bayan wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai hari kauyen, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin tsoro da firgici.

Yadda aka ceto mutanen Zamfara da aka sace

Majiyoyi sun bayyana cewa an samu nasarar ceto mutanen ne da misalin karfe 4:00 na yamma, sakamakon matsin lamba mai tsanani da jami’an tsaro na hadin gwiwa suka yi wa 'yan bindiga a yankin Moriki.

A cewar majiyoyin, aikin ceton ya samu nasara ne bayan hadin kai da tsare-tsaren jami’an tsaro da aka tura yankin, wanda ya tilasta wa ‘yan bindigan barin mutanen da suka sace sannan suka tsere.

“An ceto dukkan mutanen 20 cikin koshin lafiya ba tare da wani rauni ba. An kai su asibitin gwamnati domin duba lafiyarsu, daga bisani aka yi musu tambayoyi kafin a mika su ga iyalansu."

- Wata majiya

Jami'an tsaro na ci gaba da sintiri

Sun kara da cewa an kara kaimi wajen sintiri na hadin gwiwa a yankin, domin hana sake aukuwar hare-hare tare da taimakawa wajen yiwuwar ceto wasu da aka sace a kauyuka makwabta.

Kara karanta wannan

Matakin da gwamnati ta ɗauka bayan ƴan ta'adda sun kashe fiye da mutum 30 a Neja

Mazauna kauyen Dunfawa sun bayyana jin dadinsu bisa samun nasarar ceton mutanen, tare da rokon hukumomi da su ci gaba da tsaurara tsaro domin hana sake faruwar sace-sace a gaba.

Jami'an tsaro sun ragargaji 'yan bindiga a Zamfara
Taswirar jihar Zamfara, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga

'Yan ta'adda sun farmaki 'yan sanda

A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan ta'adda dauke da makamai sun kai hari kan wani shingen binciken 'yan sanda a jihar Neja.

Yan ta'addan wadanda suka zo kan babura, sun kai harin ne a kauyen New Kalli da ke karamar hukumar Borgu a jihar Neja.

Maharan sun kona masaukin jami’an tsaro, suka lalata amfanin gona na manoma tare da kwashe wasu kayayyakin kafin su tsere.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng