Israila Ta Shiga Batun Muzgunawa Kiristoci a Najeriya, Netanyahu Ya Fadi Shirin da Yake Yi

Israila Ta Shiga Batun Muzgunawa Kiristoci a Najeriya, Netanyahu Ya Fadi Shirin da Yake Yi

  • Firaministan Israila, Benjamin Netanyahu, ya yi tsokaci kan batun muzgunawa Kiristoci a sassan daban-daban na duniya
  • Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa ana muzgunawa Kiristoci a Najeriya kuma a shirye yake ya taimaka musu
  • Firaministan na Israila dai ya bayyana kasarsa a matsayin wadda ta fi kowace kasa ba al'ummar Kiristoci kariya a duniya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Amurka - Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya yi magana kan batun muzgunawa Kiristoci a Najeriya.

Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa kasarsa na aiki a kan wani tsari na musamman domin tallafa wa al’ummomin Kiristoci da ke fuskantar matsin lamba a Najeriya.

Netanyahu zai taimakawa Kiristoci a Najeriya
Benjamin Netanyahu da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu Hoto: @netanyahu, @aonanuga1956
Source: Twitter

Netanyahu ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wani taro da jagororin al’ummar Kiristocin Evangelical a jihar Florida ta Amurka kamar yadda ya sanya a shafinsa na X.

Shugaban Israila na son kare Kiristoci

Kara karanta wannan

An yi wa Netanyahu taron dangi kan yunkurin kawo dauki ga Kiristoci a Najeriya

Firaministan ya bayyana Isra’ila a matsayin kasar da ta fi kowa iya kare Kiristoci a duniya.

"Ina ganin yakin da ake yi da mu da kuma yakin da ake yi da al’adunmu na Yahudawa da Kiristoci, ana gwabza shi a ko’ina cikin duniya."
"Kuma ana yin wannan yaki ne musamman ta hanyar kungiyoyi biyu, masu sattsauran ra’ayin Shi’a da kuma masu tsattsauran ra’ayin Sunni.”
“Hakan na nufin wata tawaga da Iran ke jagoranta, wadda aka raunana kwarai amma har yanzu tana nan, da kuma tawagar Sunni da Muslim Brotherhood ke jagoranta, wadda ta bazu ko’ina.”

- Benjamin Netanyahu

Netanyahu ya yi zargi kan muzgunawa Kiristoci

Netanyahu ya ce waɗannan kungiyoyi suna shiga Turai, Amurka da Afirka, har da Najeriya, inda ya ce suna sane da cewa ana tsananta wa Kiristoci a sassa daban-daban na duniya.

“Muna sane da cewa ana tsananta wa Kiristoci a Gabas ta Tsakiya, a Siriya, a Lebanon, a Najeriya, a Turkiyya da sauran wurare."
"Mun san, kamar yadda ku ma kuka sani, cewa kasa guda ɗaya ce ke kare al’ummar Kiristoci, tana ba su damar bunkasa, tana kare su, tana tabbatar da cewa suna rayuwa lafiya kuma wannan kasa ita ce Isra’ila. Babu wata kasa daban. Babu."

Kara karanta wannan

'Shugaba Bola Tinubu zai sanya wa Najeriya sabon suna'

- Benjamin Netanyahu

Wane shiri Israila ke yi?

Netanyahu ya ce Isra’ila na shiga wani yunkuri na haɗa kasashe masu goyon bayan al’ummomin Kiristoci a duniya, musamman waɗanda ke cikin mawuyacin hali kuma suka cancanci taimako.

“Yadda kuke taimaka mana, haka ma mu muna son taimaka muku. Kuma muna da ikon yin hakan. A Afirka, ta hanyar bayanan sirri, a Gabas ta Tsakiya, ta hanyoyi da dama da ba zan lissafo su ɗaya bayan ɗaya ba."

- Benjamin Netanyahu

Ya ce wannan ne babbar ajandar Isra’ila, kuma muhimmin ɓangare ne na manufofinta.

Netanyahu ya ce ana muzgunawa Kiristoci a Najeriya
Benjamin Netanyahu a wajen taro da Kiristoci a Amurka Hoto: @netanyahu
Source: Twitter

Netanyahu ya gana da Trump

Jawabin Netanyahu ya zo ne kwana guda bayan ganawarsa da shugaban Amurka, Donald Trump, wanda ya sanar da kai hare-haren sama a Najeriya a ranar Kirsimeti.

A ranar da aka kai hare-haren, Netanyahu ya ce dole a kawo karshen hare-haren da ake kai wa Kiristoci a Najeriya.

Isra’ila ita ce kasa guda tilo da ta fito fili ta mara wa Amurka baya kan ikirarin cewa ana tsananta wa Kiristoci a Najeriya.

Kara karanta wannan

Jerin kungiyoyin 'yan ta'adda 8 da Amurka ta fi damuwa da ayyukansu a Najeriya da Afirka

Kasashen biyu dai abokan hulɗa ne na kud-da-kud a fannin siyasa da tsaro.

Akwai wata a kasa

Sabitu Usman ya shaidawa Legit Hausa cewa kalaman Benjaminn Netanyahu abin Allah wadai ne.

Ya bayyana cewa Netanyahu bai da idon da zai kalli mutane ya ce wai yana son kare Kiristoci duba da irin barnar da ya yi a Gaza.

"Akwai mamaki cewa wai Netanyahu ne yake batun kare Kiristoci a Najeriya duk da irin kisan kiyashin da ya yi a Gaza."
"Mutumin da kotun ICC ke nema kan zargin kisan kare dangi bai da hurumin cewa zai kare Kiristoci, wadanda suna daga cikin mutanen da ya rika kashewa a Falasdinu."

- Sabitu Usman

Israila ta yi kira ga 'yan Najeriya

A wani labarin kuma, kun ji cewa Jakadan Israila a Najeriya, Michael Freeman, ya aika sako na musamman ga 'yan Najeriya.

Michael Freeman ya yi kira ga 'yan Najeriya da su rungumi zaman lafiya da juna ba tare da nuna bambanci ba.

Jakadan na Israila ya bukaci a zauna cikin fahimtar juna da girmama kowa, ba tare da la’akari da bambance-bambancen addini ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng