An Jefa Kwamishinan Bauchi a Gidan Yari, Ana Zarginsa da Daukar Nauyin Ta'addanci
- Hukumar EFCC ta gurfanar da wani kwamishinan Bauchi kan zargin karkatar da dalar Amurka miliyan tara domin daukar nauyin ta'addanci
- Ana zargin kwamishinan ya tura kudaden ga shugaban Miyetti Allah, Bello Bodejo, bayan ya canja kudaden gwamnatin Bauchi zuwa dala
- Kotu tura kwamishinan da ake zargi zuwa gidan yari, tare da sanya lokacin da za a saurari bukatar ba da belinsa da na wasu mutane uku
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Hukumar yaƙi da yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) ta gurfanar da kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja ranar Laraba.
EFCC ta gurfanar da Yakubu Adamu ne tare da wasu mutane uku, Balarabe Abdullahi Ilelah, Aminu Mohammed Bose, da Kabiru Yahaya Mohammed.

Source: Twitter
Zargin kwamishina da daukar nauyin ta'addanci
Hukumar ta tuhumar kwamishinan da mutanen uku ne kan zarge-zarge guda 10 da suka shafi kashe dalar Amurka miliyan 9.7 a wajen daukar nauyin ta’addanci, in ji rahoton The Cable.
Sai dai, waɗanda ake tuhumar sun bayyana cewa ba su aikata dukkan tuhume-tuhumen da ake yi masu ba a gaban Mai shari’a Emeka Nwite.
A cewar EFCC, kwamishinan da sauran mutanen sun haɗa baki wajen samar da tsabar kuɗi har dalar Amurka miliyan 2.3 domin amfanin shugaban ƙungiyar Miyetti Allah, Bello Bodejo, da wasu mutane da ke da alaƙa da shi, bisa amincewar gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed.
Hukumar ta bayyana cewa an yi amfani da waɗannan kuɗaɗen wajen tallafa wa ƙungiyar ta’addanci, wanda hakan ya saɓa wa dokar kariya da haramta ta’addanci ta shekarar 2022.
Takaddama kan ba da belin kwamishina
Lauyan waɗanda ake tuhuma, Gordy Uche (SAN), ya roƙi kotun da ta ba da su beli, inda ya bayyana cewa tuhume-tuhumen ba su nuna alaƙa ta zahiri tsakanin kuɗin da aka ce an kashe da ayyukan ta'addanci ba.
Ya kuma ƙara da cewa ci gaba da tsare kwamishinan kudi, Yakubu Adamu yana shafar biyan albashin ma'aikatan jihar Bauchi kusan 600,000.
Sai dai, lauyan EFCC, Samuel Chime, ya yi adawa da buƙatar belin, yana mai nuna girman laifin da kuma gaskiyar cewa Kwamishinan yana fuskantar wata shari'ar halatta kuɗin haram ta daban.

Source: UGC
An jefa kwamishina a gidan yarin Kuje
Mai Shari’a Nwite ya ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 5 ga watan Janairu, 2026, domin yanke shawara kan buƙatar belin wadanda ake kara.
Sannan ya bayar da umarnin a tsare waɗanda ake tuhumar a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja, kamar yadda rahoton Punch ya nuna.
EFCC ta kuma zargi Kwamishinan da ɓoye asalin kuɗaɗen gwamnatin jihar Bauchi ta hanyar amfani da ‘yan canji (BDC) domin mayar da su dalar Amurka don gudanar da ayyukan da suka saɓa wa doka.
An roki Gwamna Bala ya bar EFCC sun yi aikinsu
Wata kungiyar matasan jam’iyyar APC, a Arewa maso Gabas (APC-YPNE), ta bukaci gwamnan jihar, Bala Mohammed, da ya kyale hukumar EFCC ta gudanar da bincikenta kan zarge-zargen da ake yi wa kwamishinan.

Kara karanta wannan
Jerin kungiyoyin 'yan ta'adda 8 da Amurka ta fi damuwa da ayyukansu a Najeriya da Afirka
A zantawarsa da Legit Hausa, shugaban kungiyar, Kabiru Garba Kobi, ya ce ta hanyar sahihin bincike da EFCC ke gudanarwa ne kawai za a gano gaskiya game da kudaden da aka karkatar.
"Ga duk mai hankali ya san wannan babu siyasa a ciki. Tuhume-tuhume ne aka gabatar bayan bincike, to ka ga a nan dan jarida, ai sai a bari kotu ta yanke hukunci bayan sauraron kowane bangare.
"Kowa dai ya san EFCC ba za ta yin kwanta sai da zakara. To tun da kuwa haka ne, ai bai kamata shi mai girma gwamna ya daga hankalinsa, har ya fito yana cewa ana masa bita da kulli ba.
"Cewar wai zai kai korafi gaban wasu hukumomi har ma da kasashen waje kan lamarin nan, zai sanya mutane su diga masa ayar tambaya, in ba rami me ya kawo zancen rami? Ai ciki da gaskiya, wuka ba ta huda shi."
Kabiru Garba Kobi ya kuma yabawa yadda EFCC ta mayar da hankali kan bincikenta, yana mai cewa al'ummar bauchi na son sanin yadda aka tafiyar da kudin jihar ta wannan fuska.
Wani zargi da ake yi wa kwamishinan Bauchi
Tun da fari, Legit Hausa ta ruwaito cewa, hukumar EFCC ta gurfanar da kwamishinan kudin jihar Bauchi, Yakubu Adamu bisa zargin ya karkatar da fiye da Naira biliyan biyar.
Ana zargin Yakubu Adamu ya karkatar da biliyoyin kudin da aka fitar don sayen wasu baburan gwamnati kafin Gwamna Bala Mohammed ya nada shi mukamin kwamishina.
Zarge-zargen da ake yi wa kwamishinan kudi da kamfanin sun shafi karkatarwa da halatta kuɗin haram da jimillarsu ta kai Naira biliyan 5.79, wadanda ya musanta su duka.
Asali: Legit.ng


