Sheikh Ahmad Gumi Ya Maka Wasu Mutum 2 a Kotu kan Rubutun da Suka Yi a Facebook

Sheikh Ahmad Gumi Ya Maka Wasu Mutum 2 a Kotu kan Rubutun da Suka Yi a Facebook

  • Babban malamin addinin musulunci mazaunin Kaduna, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi ya kai karar wasu mutum biyu gaban kotu
  • Malam Ahmad Gumi ya kai karar mutanen kotu ne bisa wani rubutu da suka yi Facebook, kuma suka jingina masa
  • Lauyan Sheikh Gumi, Suleiman Lere, ya ce ya kamata wannan shari’ar ta zama darasi ga masu amfani da kafafen sada zumunta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna, Nigeria - Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya shigar da ƙara gaban Kotun Majistare da ke Jihar Kaduna a kan wasu masu amfani da Facebook.

Sheikh Ahmad Gumi ya kai karar mutanen biyu ne bisa zargin haɗin baki wajen aikata laifi da wallafa rubuce-rubucen ɓatanci da aka jingina masa ƙarya.

Sheikh Ahmad Gumi.
Babban malamin addinin musulunci mazaunin Kaduna, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi Hoto: Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi
Source: Facebook

Sunayen wadanda Sheikh Gumi ya kai kara

Premium Times ta ce karar, mai lamba KMD/685/25, wadda aka shigar a ranar Laraba, ta bayyana George Udom da Bello Isiaka a matsayin waɗanda ake ƙara, yayin da Sheikh Gumi shi ne mai ƙara.

Kara karanta wannan

Tinubu ya tura tawaga Morocco yayin da Najeriya za ta fafata da Tanzania a AFCON 2025

A cewar takardun kotu, ana zargin waɗanda ake ƙarar da wallafa wani saƙo a Facebook a ranar 23 ga Disamba, 2025, inda suka jingina wa Sheikh Gumi wasu maganganu.

Ana tuhumar mutanen biyu da kirkirar karya tare da jinginawa Shekh Gumi, inda suka yi ikirarin shi ya fadi kalaman ga Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa.

Wane laifi 'yan Facebook suka aikata?

Saƙon da wadanda ake zargin suka wallafa, suka yi ikirarin Sheikh Ahmad Gumi ne ya fada, shi ne:

“Idan Ministan Tsaro Christopher Musa bai dakatar da hare-haren sojoji kan ’yan bindiga ba, za a hallaka dukkan iyalinsa da ke Zango Kataf a Kudancin Kaduna.”

A cikin ƙarar da ya shigar, Sheikh Gumi ya ce rubutun ya nuna tamkar shi ne ya yi barazana ga wani babban jami’in gwamnati da kundin tsarin mulki ya ɗora masa alhakin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a Najeriya.

Sheikh Gumi ua musanta fadar kalaman

Ta bakin lauyansa, Suleiman Lere, Sheikh Gumi ya musanta rubutawa ko amincewa da wannan saƙo, inda ya bayyana shi a matsayin “ƙage, rashin hankali da aka tsara shi da gangan.”

Kara karanta wannan

Rawani ya fadi: Kotu ta yanke wa basarake da wani mutum 1 hukuncin kisa a Gombe

Ya ce wallafar ta yi mummunar illa ga mutuncinsa a matsayin malami da aka sani da wa’azin zaman lafiya, tattaunawa da kauce wa tashin hankali, tare da jefa shi cikin barazana.

Babban malamin ya kuma bayyana cewa jingina masa kalaman na iya jefa rayuwarsa cikin haɗari, domin irin waɗannan zarge-zarge na iya haddasa kai masa hari ko kuma janyo masa matakan da ba su dace ba daga hukumomin gwamnati.

Sheikh Ahmad Gumi.
Fitaccen malamin addinin islama a Najeriya, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi. Hoto: Dr. Ahamd Abubakar Gumi
Source: Facebook

Da yake magana kan shari’ar, lauyan Sheikh Gumi, Suleiman Lere, ya ce shari’ar ya kamata ta zama darasi ga masu amfani da kafafen sada zumunta da ke yaɗa ƙarya da ɓatanci.

Ya ce:

“Lokacin da mutane ke ɓoye kansu ta wayar hannu domin lalata mutuncin wasu ya wuce.”

Sakon Sheikh Gumi ga ministan tsaro

A wani labarin, kun ji cewa Sheikh Ahmad Abubakar Gumi ya bayyana cewa ba ya goyon bayan duk wani tsari da zai bai wa ’yan bindiga damar ci gaba da aikata ta’addanci.

Sheikh Gumi ya yi tsokaci kan kalaman sabon ministan tsaron Najeriya, Janar CG Musa (mai ritaya), wanda ya ce babu sasanci da ’yan bindiga.

Malamin ya bayyana cewa wannan matsaya ta yi daidai da tsarin da ya dace da aikin soja, domin ya nuna ƙarfin gwamnati da ƙudirinta na kawo ƙarshen ta’addanci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262