Kungiyar CAN Ta Yi Magana da Babbar Murya ga Tinubu yayin da Ake Shirin Kirsimeti a Najeiya

Kungiyar CAN Ta Yi Magana da Babbar Murya ga Tinubu yayin da Ake Shirin Kirsimeti a Najeiya

  • Kungiyar CAN ta nuna matukar damuwa kan karuwar matsalolin rashin tsaro a sassa daban-daban na Najeriya
  • Shugaban CAN a Arewa ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro ta sanya Kiristoci da dama sun sanya shakku kan bukukuwan Kirsimeti
  • YakubuPam ya bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnonin jihohi su tashi tsaye domin kawo karshen matsalar

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) a Arewa ta yi muhimman kira ga gwamnatin tarayya da kuma gwamnonin jihohi kan matsalar rashin tsaro.

Kungiyar CAN ta bukaci gwamnatin tarayya da na jihohi da su karfafa tsarin tsaro a kasar nan a duk tsawon lokacin bukukuwan Kirsimeti.

Kungiyar CAN ta yi kira ga Shugaba Bola Tinubu
Shugaban kasar Najeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Hoto: @DOlusegun
Source: Facebook

Jaridar TheCable ta ce shugaban CAN na Arewa, Yakubu Pam, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, 18 ga watan Disamban 2025.

Kara karanta wannan

Bayan suka ta ko ina, an dakatar da yi wa dogarin Shugaba Tinubu karin girma

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

CAN ta koka kan rashin tsaro

Yakubu Pam ya ce karuwar rashin tsaro a kasar nan na jefa shakku kan shagulgulan Kirsimeti a al’ummomi da dama a Najeriya.

"Kiristoci da dama suna tunanin za su zauna a inda suke ba tare da yin tafiye-tafiye ba, saboda tsoron lafiyarsu, ganin yadda manyan hanyoyi, yankunan karkara, har ma da wuraren ibada suka zama wuraren da ake kai hare-haren tashin hankali.”

- Yakubu Pam

Shugaban na kungiyar CAN ya ce kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya na ci gaba da kasancewa ginshiki mai muhimmanci ga haɗin kan kasa da zaman lafiyar al’umma.

Wane kira CAN ta yi ga gwamnati?

Yakubu Pam ya jaddada cewa wajibi ne gwamnatin tarayya ta tura jami’an tsaro zuwa yankunan da ke cikin haɗari a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

"Yayin da duniya ke shagulgulan wannan lokaci, ina kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnonin jihohin Arewa da Ministan Abuja da su ɗauki matakai cikin gaggawa, domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a lokacin bukukuwan da ma bayan su.”

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya yi wa 'yan Najeriya albishir kan matsalar rashin tsaro

"Kalubalen tsaro da ke addabar kasar nan a baya-bayan nan, musamman karuwar ayyukan ’yan bindiga, ’yan ta’adda da sauran kungiyoyin masu aikata laifuka a sassa da dama na Arewacin Najeriya, abin damuwa ne matuka.”

- Yakubu Pam

Yakubu Pam ya bayyana cewa Kirsimeti na nuni da bikin haihuwar Yesu Almasihu, wanda a al’ada ake yi da taron iyalai, ibada da ayyukan soyayya da taimako, amma a wannan karon karuwar rashin tsaro na barazana ga wadannan bukukuwa.

CAN ta bukaci Tinubu ya magance rashin tsaro
Shugaban kungiyar CAN a yankin Arewa, Yakubu Pam Hoto: Plateau Update
Source: Facebook

CAN ba za ta lamunci rashin tsaro ba

"Ba za mu amince da hakan ba a kasar da ke da dimokuraɗiyya, inda ya kamata a kiyaye ’yancin zirga-zirga, ibada da cudanya da jama'a."
"Muna kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi 19 na Arewa da su nuna jajircewa wajen sauke nauyin da ke kansu ta hanyar karfafa tsarin tsaro."
"Inganta ayyukan tattara bayanan sirri, da kuma tura isassun jami’an tsaro zuwa yankunan da ke cikin haɗari, manyan hanyoyi, wuraren ibada da wuraren taruwar jama’a a duk tsawon lokacin bukukuwan Kirsimeti.”

- Yakubu Pam

CAN ta yi ta'aziyyar Dahiru Bauchi

A wani labarin kuma kun ji cewa kungiyar CAN reshen jihohin Arewa ta nuna alhininta kan rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Kara karanta wannan

Tinubu ya sa labule da hafsoshin tsaro bayan amincewa da tura sojoji Benin

Kungiyar CAN ta bayyana cewa rasuwar malamin ta bar babban gibi ga harkokin zaman lafiya da tarbiyya, musamman a Arewacin ƙasar.

Hakazalika, kungiyar CAN ta ce Sheikh Dahiru Bauchi ya shafe tsawon rayuwarsa yana ba da gudummawa wajen bunƙasa karatun Alƙur’ani.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng