Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed da Takwaransa na NUPRC Sun Yi Murabus

Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed da Takwaransa na NUPRC Sun Yi Murabus

  • Shugaban hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed da takwaransa na hukumar NUPRC, Gbenga Komolafe sun yi murabus daga kan mukamansu
  • Hakan na zuwa ne bayan shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya zargi Farouk Lawal da wadaka da kudi fiye da abin da yake samu
  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tura sunayen mutum biyu da za su maye gurbinsu ga Majalisar Dattawa domin tabbatar da nadinsu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Kasa (NMDPRA), Farouk Ahmed ya yi murabus daga mukaminsa yau Laraba, 17 ga watan Disamba, 2025.

Kara karanta wannan

Monguno ya tona yadda aka dakile shi a mulkin Buhari, ya kira sunayen mutum 2

Wannan na zuwa ne bayan shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote, Aliko Dangote ya yi zargin cewa shugaban hukumar NMDPRA na biya wa ƴaƴansa guda huɗu kuɗin makaranta a Switzerland da suka kai dala miliyan 5.

Shugaban hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed.
Tsohon shugaban hukumar NMDPRA ta kasa, Farouk Ahmed Hoto: @aonanuga1956
Source: Facebook

Farouk Ahmed ya yi murabus

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya tabbatar da murabus din Farouk Ahmed a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Haka zalika, shugaban hukumar NUPRC, wacce ita ma ta shafi kula da harkokin man fetur, Gbenga Komolafe ya yi murabus daga mukaminsa nan take.

Onanuga ya ce Shugaba Bola Tinubu ya tura sunayen mutane biyu zuwa Majalisar Dattawa domin maye gurbinsu.

Shugaba Tinubu ya maye gurbinsu

Shugaban kasar ya rubuta wasika zuwa Majalisar Dattawa, yana rokon a gaggauta tantancewa da amincewa da Oritsemeyiwa Eyesan a matsayin shugaban NUPRC, da kuma Saidu Mohammed a matsayin shugaban NMDPRA.

Sanarwar ta ce, "Wadanda aka nada guda biyu kwararru ne a fannin harkokin mai da iskar gas."

Sa'o'i kafin murabus dinsa, tsohon shugaban NMDPRA ya ziyarci Shugaba Bola Tinubu a fadar shugaban kasa da ke babban birnin tarayya, Abuja.

Kara karanta wannan

Majalisar wakilai ta shiga dambarwar Dangote da shugaban NMDPRA

Tinubu ya gana da tsohon shugaban NMDPRA

Sanye da kayan gargajiya, Farouk Ahmed ya shafe kasa da mintuna 30 yana ganawa da Bola Tinubu kafin ya bar harabar Aso Rock.

Babu wata sanarwa a hukumance daga fadar shugaban kasa kan dalilin ganawar Tinubu da Farouk Ahmed, kuma ko da ya fito, bai tsaya ya yi magana da manema labarai na.

Farouk Ahmed da Gbenga Komolafe
Tsohon shugaban NUPRC, Gbenga Komolafe da takwaransa tsohon shugaban NMDPRA, Farouk Ahmed Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Tashar Channel tv ta tattaro cewa lokacin da tsohon shugaban NMDPRA ya fito daga ofishin shugaban kasa, ya ce lokacin tashi aiki ya yi, don haka ba zai ce uffan ba.

"Yamma ta yi ba zai yiwu na tsaya hira da manema labarai ba. Yanzu karfe 5:00 na yamma ta wuce, don haka lokacin tashi daga aiki ya yi," in ji Farouk Ahmed.

Farouk Ahmed ya maida martani ga Dangote?

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon shugaban NMDPRA, Injiniya Farouk Ahmed, ya musanta wata sanarwa da ake cewa ya fitar kan zarge-zargen da ake yi masa.

Kara karanta wannan

Ana rade-radin DSS ta cafke malamin Musulunci kan zanga zanga game da Falasdinu

Farouk Ahmed ya bayyana cewa yana sane da zarge-zargen da Dangote ya masa tare da iyalansa, wadanda ya bayyana a matsayin marasa tushe.

Ya ce yana da yakinin cewa binciken da ake gudanarwa zai taimaka wajen warware dukkannin shakku da kuma wanke sunansa daga duk wani zargi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262